Yan ta'adda
Gwamnatin Kogi ta rufe kasuwanni da tashoshin mota a kananan hukumomi 7 don yakar ƴan bindiga. Sanarwar Kingsley Fanwo ta ce an ɗauki matakin ne na dan wani lokaci.
'Yan bindiga da ke alaka da Bello Turji sun kai hari a kauyen Kiratawa a Sokoto, inda suka kashe limamin gari, jami'an tsaro sun isa yakin don tsare al'umma.
Rahotanni sun nuna cewa yan ta'addan da suka kashe musulmai sama da 100 a jihar Kwara sun yi amfani da masallaci, sun kashe duk wanda ya zo Sallah.
Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya isa jihar Kwara domin jaje da tattaunawa da hukumomi bayan kisan Musulmi kusan 200 da yan ta'adda suka yi.
Rahotanni sun bayyana yadda yan ta’adda suka aika wasiƙa ga al’ummar Nuru da Woro a Kwara, suna sanar da niyyarsu ta wa’azi kafin kai hari mai muni.
Shugaban karamar hukumar Kaiama a Kwara ya bayyana cewa masu bayar da bayanan sirri wa 'yan ta'adda sun taimaka wajen kisan gillar da aka yi wa Musulmai a Kwara
Wasu 'yan ta'addan kungiyar Boko Haram sun kai harin kwanton bauna kan dakarun sojojin Najeriya a jihar Borno. Harin ya jawo an samu asarar rayukan sojoji.
Dan ta'addan Boko Haram mai alaka da Abubakar Shekau da ake kira Abubakar Saidu da aka fi sani da Sadiku ne ya jagoranci kashe Musulmai kusan 200 a Kwara.
'Yan bindiga sun kashe mutum 13 a kasuwar Anwase, Benue, sannan suka sace mata. Wannan hari ya biyo bayan kisan mutum 16 a Abande kwanaki biyu da suka wuce.
Yan ta'adda
Samu kari