"Ni Bawan Talakawa Ne," Gwamna Ya Soki Wasu Manya bayan Ganawa da Tinubu

"Ni Bawan Talakawa Ne," Gwamna Ya Soki Wasu Manya bayan Ganawa da Tinubu

  • Gwamna Hyacinth Alia na jihar Benuwai ya ce al'umma ne suka zaɓe shi kuma su zai yi wa aiki ba wasu tsirarun mutane ba
  • Gwamna Alia ya bayyana haka ne da yake hira da ƴan jarida a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja bayan ganawa da Bola Tinubu
  • Ya ce gwamnatinsa ta maida hankali wajen tallafawa mutane musamaman matasa domin gina masu gobe mai kyau a Benuwai

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Benue - Gwamna Hyacinth Alia na Benuwai ya ce gwamnatinsa ta maida hankali wajen samar da shugabanci na gari ga al’umma ba wai gina wasu tsirarun mutane ba.

Gwamna Alia ya ce al'umma ce a gabansa kuma su yake yi wa aiki ba wasu tsirararun mutane da ke kallon kansu a matsayin wasu manya ba.

Kara karanta wannan

Tinubu na shirin rusa wata ma'aikata, an matsa masa lamba ya kori wasu ministoci

Gwamna Alia na jihar Benuwai.
Gwamnan jihar Benuwai ya ce al'umma ne a gabansa ba wasu tsirarun mutane ba Hoto: Fr. Hyacinth Lormem Alia
Asali: Facebook

Gwamna Alia ya gana da Bola Tinubu

Ya faɗi haka ne yayin zantawa da manema labarai jim kadan bayan ganawa da shugaban kasa Bola Tinubu a fadar gwamnati da ke Abuja, Channels tv ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnan ya ce ya je fadar shugaban ƙasa ne domin yi wa shugaba Tinubu bayani kan al’amuran jihar Binuwai, musamman matsalar tsaro.

Gwamna Alia ya faɗi abin da ke gabansa

A cewar Gwamna Alia, talakawan ne suka zabe shi domin ya yi musu hidima kuma sune a gabansa ba wai masu daukar kansu a matsayin masu ƙarfin iko a jihar Benuwai ba.

"Mutane na zo na yiwa aiki, ban san su waye manya ba, al'umma ta kawo ni kan wannan kujera shiyasa duk abin da ya shafe su nake ɗaukarsa da gaske, idan shugaba ya zama bawan talakawansa komai na tafiya daidai."

Kara karanta wannan

"In Sha Allahu za mu ɗinke ɓaraka," Gwamna ya gano waɗanda suka haddasa rikici a PDP

"Na san zafin da suke ji amma abin ya fi kamata shi ne su ɗauki lamarin da sauki su sauƙaƙawa kansu da kuma talakawa," in ji Alia.

Gwamma ya fara ba matasa tallafi

Gwamnan ya kuma bayyana cewa a yanzu gwamnatinsa na maida hankali ne wajen bai wa al’ummar jihar Binuwai, musamman matasa tallafi, Daily Post ta rahoto.

Ya ce sama da matasa 10,000 ne ake horas da su sana’o’in zamani yanzi haka kuma gwamnatin Benuwai ta ɗauki nauyin matasa zuwa kasar Sin domin koyon sana’o’i.

Tsagin APC a Benue ya soki Gwamna Alia

A wani rahoton kuma jam'iyyar APC ta caccaki Gwamna Alia Hyacinth na Benue kan rikicin siyasar cikin gidan a jihar da ke faruwa

Mambobin APC a Majalisar Tarayya su suka zargi gwamnan da neman ruguza jam'iyyar domin biyan buƙatar kansa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: