Katsina: Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yanke Hukuncin Ƙarshe Kan Kujarar Ɗan Majalisar Tarayya

Katsina: Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yanke Hukuncin Ƙarshe Kan Kujarar Ɗan Majalisar Tarayya

  • Kotun ɗaukaka ƙara mai zama a Abuja ta kawo karshen taƙaddama kan kujerar ɗan majalisar Faskari, Kankara da Sabuwa
  • Kwamitin alkalan kotun ya tabbatar da Hon Shehu Ɗalhatu Tafoki a matsayin sahihin wanda ya lashen zaben da aka yi a 2023
  • Tafoki, tsohon mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Katsina ya sha fama da shari'a tun bayan zaɓen fidda gwani a APC

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina - Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da Shehu Dalhatu Tafoki a matsayin halastaccen ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Faskari/Kankara/Sabuwa a Katsina.

Kotun ta sanar da haka ne yayin yanke hukunci kan ƙarar da ɗan takarar PDP, Jamilu Mohammed ya shigar gabanta ya na kalubalantar nasarar Tafoki.

Kara karanta wannan

"Muna kan aiki," Gwamna ya faɗi matakin da ya ɗauka kan biyan sabon albashin N70,000

Kotun daukaka kara.
Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da nasarar ɗan majalisar Faskari, Sabuwa da Kankara, Hon. Tafoki Hoto: Court of Appeal
Asali: Facebook

Kotun daukaka kara mai zama a Abuja ta amince da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta yanke tun farko, wanda ya tabbatar da nasarar Tafoki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahoton Leadership ya kawo cewa dukkan alƙalai uku da suka saurari shari'ar sun gamsu cewa babu wani kuskure a hukuncin da kotun zaɓe ta yanke.

Yadda Tafoki ya yi fama da shari'a

Hukuncin ya raba gardama kan taƙaddamar da ta shafe watanni 27 ana yi game da kujerar ɗan majalisar Faskari/Kankara/Sabuwa a jihar Katsina.

Tafoki ya fara fuskantar ƙalubale ne tun daga zaɓen fidda gwani na PDP, inda abokin karawarsa, Murtala Isah Kankara ya maka shi a kotu, rahoton Daily Trust.

Sai dai daga ƙarshe kotun ƙoli ta warware rigimar a lokacin da ta tabbatar da Shehu Ɗanhatu Tafoki a matsayin sahihin ɗan takarar APC.

Kara karanta wannan

'Yan ta'adda masu yawa sun sheka barzahu bayan sojoji sun yi musu ruwan wuta

A halin yanzu dai bayan shafe dogon lokaci yana fuskantar shari'a a kotu, Shehu Ɗalhatu Tafoki ya zama halastaccen ɗan majalisar Kankara, Faskari da Sabuwa.

Hon Tafoki ya yabawa Dikko Raɗɗa

Bayan yanke hukuncin karshe na kotun ɗaukaka ƙara, Hon. Tafoki ya godewa Allah tare da godewa gwamnan Katsina Mallam Dikko Umaru Radda bisa irin goyon bayan da ya ba shi.

Ya sha aƙwashin maida hankali kan ayyukasa na majalisa kuma ya ba da tabbacin cewa zai yi kokarin zuba ayyuka fiye da waɗanda ya yi a matsayin mataimakin kakakin majalisar Katsina.

2027: Ayodele ya ba ƴan adawa shawara

A wani rahoton Primate Elijah Ayodele ya bayyana dabarun da ya kamata ƴan adawa su yi idan suna son kayar da jam'iyya mai mulki a babban zaɓe na gaba.

Fitaccen limamin cocin ya faɗi dabarun ne a lokacin da ƴan siyasa suka fara shirye-shiryen zaɓen 2027 a Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262