Jami'an Tsaro Sun Tono Bama Bamai a Garuruwa da Dama a Arewacin Najeriya

Jami'an Tsaro Sun Tono Bama Bamai a Garuruwa da Dama a Arewacin Najeriya

  • Jami'an tsaro sun tono abubuwan fashewa da bama-bamai a garuruwa daban daban a wasu sassan jihar Neja
  • Mai magana yawun ƴan sanda, SP Wasiu Abiodun ya ce sun gano waɗannan miyagun makamai ne tsakanin 2021 zuwa 2023
  • Ya ce tuni jami'an ƴan sanda na sashin kwance bama-bamai suka lalata su a ranar 22 ga watan Agusta, 2024

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Niger - Jami'an tsaro sun tono wasu abubuwan fashewa da bama-bamai a wurare daban-daban a wasu sassan jihar Neja.

Daga cikin wuraren da aka tono bama-baman har da Galadima-Kogo da ke ƙaramar hukumar Shiroro, Mutun-ɗaya a Mangu da unguwar Gbeganu a Minna.

Taswirar jihar Neja.
Jami'an tsaro sun tono tare da lalata bama-bamai a jihar Niger Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Jami'in hulda da jama'a na rundunar ƴan sanda reshen jihar Neja, SP Wasiu Abiodun ne ya tabbatar da haka a wata sanarwa ranar Litinin, Daiy Trust ta tattaro.

Kara karanta wannan

Ana fama da yunwa, ambaliyar ruwa ta yi ɓarna a gonakin mutane a jihohi 2 na Arewa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda jami'an tsaro suna tono bama-bamai

Ya ce jami'ai sun gano ababen fashewar ne a lokacin ayyukan yaki da ta'addanci tsakanin shekarar 2021 zuwa 2023 a jihar da ke Arewa ta Tsakiya.

A karamar hukumar Shiroro, musamman Galadima-Kogo tashin bam ya yi mummunar ɓarna a 2022, wanda ya yi sanadin asarar jami’an tsaro na NSCDC.

Rundunar hadin gwiwa ta ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro ne suka gano wadannan bama-baman da aka boye aka binne su a wurare daban-daban a Neja.

Niger: Wane mataki daka ɗauka?

Mai magana da yawun ƴan sandan ya ƙara da cewa tuni ana lalata dukkan abubuwan fashewar da bama-baman da aka tono, Channels tv ta tattaro.

SP Wasiu Abiodun ya ce an lalata kayayyakin ne a ranar 22 ga watan Agusta, 2024, a wani wuri da ke bayan Zuma Rock, a Suleja.

Kara karanta wannan

"Ba mu da labari," Ƴan sanda su yi magana kan sace mutane 150 bayan kisan Sarkin Gobir

Babban jami'im sashin kwance bama-bamai na rundunar ƴan sandan, SP Mohammed Mamun ne ya jagoranci lalata bama-baman in ji Abiodun.

Yan bindiga sun sace darakta a Ribas

A wani rahoton kuma Ƴan bindiga sun sace wani darakta da ke aiki a hukumar tattara kuɗaden shiga ta jihar Ribas, Sir Aribibia John Fubara.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun buɗe wuta a iska kafin daga bisani su tasa abin harin su zuwa wurin da har yanzun ba a gano ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: