Ana Fama da Matsin Rayuwa, Gwamna a Arewa Ya Sayo Motocin Alfarma Sama da 10

Ana Fama da Matsin Rayuwa, Gwamna a Arewa Ya Sayo Motocin Alfarma Sama da 10

  • Domin inganta ayyukan shari'a, Gwamna Ahmed Ododo ya saya wa alƙalai sababbin motoci 11 a jihar Kogi
  • Gwamnan ya yi alkawarin cewa zai kara sayawa alkalan ƙarin motoci domin su samu damar sauke nauyin da ke kansu cikin adalci
  • Babban alƙalin jihar Kogi ya godewa gwamnan bisa cika alƙawarin da ya ɗauka na samar da motocin aiki ga akalai

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kogi - Gwamna Ahmed Usman Ododo na jihar Kogi, a ranar Talata, ya miƙawa alkalai karin motoci 11 da ya sayo masu domin sauƙaƙa aikinsu.

Gwamnan ya damƙawa babban alkalin jihar, Josiah Mejabi sababbin motocin a wani biki da aka shirya a filin Muhammad Buhari Square da ke Lokoja.

Kara karanta wannan

Gwamnatin tarayya ta fadi hanyar da za a iya raba Tinubu da mulkin Najeriya

Gwamna Ahmed Ododo.
Gwamna Ahmed Ododo ya bai wa Alƙalai motoci 11a jihar Kogi Hoto: Alhaji Ahmed Usman Ododo
Asali: Facebook

Jaridar Premium Times ta tattaro cewa yayin miƙa sababbin motocin, Gwamna Ododo ya yi alƙawarin sayo ƙarin wasu domin rabawa alƙalai su samu saukin zuwa aiki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa Gwamna Ododo ya sayo motocin?

"Wannan na cikin alƙawurran da na ɗaukarwa ma'aikatan shari'a a ranar da muka rantsar da sababbin alƙalai a watan Yuli, za mu sayo ƙarin motoci.
"A waccan ranar mun raba motoci 14 kuma a yau ga shi za mu ƙara ba da motoci 11 ga alƙalan mu masu jajircewa da aiki tuƙuru.
"Muna fatan za mu kara sayo wasu nan ba da daɗewa ba domin ba kowane alkali a faɗin jihar Kogi."

- Gwamna Ahmed Ododo.

Ahmed Ododo ya buƙaci alkalan su biya wannan karamci da gwammnati ta yi masu ta hanyar yin adalci ga duka mutanen da suna kawo masu ƙorafi a kotunan su.

Kara karanta wannan

"Yana da kyakkyawan shiri": Hadimin Tinubu ya kwantar da hankalin matasan Najeriya

Alƙalai sun godewa Gwamna Ododo

Da yake mayar da martani, babban alkalin ya gode wa gwamnan bisa cika alkawarin da ya yiwa bangaren shari’a na ba alkalai motocin aiki, Tribune Nigeria ta rahoto.

Alkalin ya ce motocin za su taimaka musu matuƙa wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata domin tabbatar da adanci da zaman lafiya a tsakanin al'umma.

Gwamnatin Katsina ta cire dokar hana fita

A wani rahoton kuma muƙaddashin gwamnan Katsina, Farouk Lawal Jobe ya cire dokar hana fita da aka sanya a ƙananan hukumomin jihar.

Sakataren gwamnatin Katsina, Abdullahi Faskari ne ya bayyana hakan ranar Talata, ya ce mutane na da damar ci gaba da harkokinsu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: