Zanga Zanga: Sojoji Sun Ci Karo da Gomman Matasa a Cikin Mota, Sun Ɗauki Mataki

Zanga Zanga: Sojoji Sun Ci Karo da Gomman Matasa a Cikin Mota, Sun Ɗauki Mataki

  • Sojoji sun kama wata babbar motar dakon kaya ɗauke da mutane 32 a garin Mararaba da ke jihar Nasarawa ranar Jumu'a
  • Wani mazaunin yankin, Adamu Yau ya ce motar ta kawo shanu ne a yayin komawa direban ya ɗauki wasu ƴan acaba da kayansu
  • Dakarun sojojin Najeriya sun nuna ba su yarda da su ba saboda zanga-zangar da ake yi kan tsadar rayuwa a faɗin ƙasar nan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Nasarawa - Jami'an sojojin da aka tura garin Mararaba a jihar Nasarawa domin su kwantar da tarzomar masu zanga-zanga sun tare wata mota maƙare da matasa.

Rahotanni sun bayyana cewa dakarun sojojin sun tare babbar motar dakon kaya ɗauke da mutane 32 a Mararaba yau Jumu'a, 9 ga watan Agusta, 2025.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai mummunan hari, sun kashe mutane sama da '30' a Arewa

Sojojin Najeriya.
Sojojin Najeriya sun tare wata babbar mata da ta ɗauko gomman mutane a jihar Nasarawa Hoto: HG Nigeiran Army
Asali: Facebook

Wani mazaunin garin Adamu Yau ya shaida wa wakilin Daily Trust cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:40 na safiyar ranar Juma’a.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mutumin ya ce tun farko direban babbar motar ya kawo shanu ne a kasuwar da ke garin kuma a hanyar komawa ya ɗauki wasu domin rage masu hanya.

Zanga-zanga: Wasu mutane ne a motar?

Adamu Ya'u ya ce daga cikin waɗanda direban ya kwasa har da ƴan acaba da baburansu da kayayyakin su.

"Wasu daga cikin fasinjojin sun fada mani cewa sun shiga motar ne domin zuwa garin Dei-Dei da ke babban birnin tarayya Abuja.
"Kuma sun zaɓi hawa motar ne don kauce wa jami’an kula da ababen hawa, wadanda suka saba kame babura a kan babbar hanyar zuwa Abuja," in ji shi.

Dalilin sojoji na kama motar

Adamu ya ƙara da cewa ga dukkan alamu dakarun sojojin sun damu da yawan waɗanda ke cikin motar ne saboda zanga-zangar da ake yi a ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Matasa sun fusata da kisan ɗan uwansu, sun bankawa fadar basarake wuta a Arewa

"Sojojin sun kama motar da karfe 8:00 na safe kuma sun umarci duka waɗanda ke ciki su sauko ƙasa, yanzu haka suna bincikarsu ɗaya bayan ɗaya."

Bayanai sun nuna sojojin na ci gaba da bincikar mutanen har zuwa ƙarfe 11:00 na safiya lokacin da aka tattara wannan rahoton, cewar Punch.

Gwamna Makinde ya musanta ikirarin Tinubu

A wani labarin kuma Gwamna Seyi Makinde ya musanta ikirarin Bola Ahmed Tinubu na rabawa jihohi N570bn domin ragewa al'umma raɗaɗin kuncin rayuwa.

Tun farko shugaban ƙasa ya ce gwamnatinsa ta rabawa gwamnoni maƙudan kuɗi domin su faɗaɗa shirye-shiryen tallafawa ƴan Najeriya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262