Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Masu Zanga Zanga, Ta Umarci Su Ci Gaba da Zama a Wurare 2

Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Masu Zanga Zanga, Ta Umarci Su Ci Gaba da Zama a Wurare 2

  • Babbar kotun jihar Legas ta ƙara yanke hukunci kan wuraren da ta amince matasa su yi zanga-zanga
  • Mai shari'a ta tsawaita umarnin cewa ba ta yarda a yi zanga zanga a ko ina ba sai wurare biyu watau Preedom Park da Peace Park
  • Ta ɗauki wannan matakin ne bayan kwamishinan shari'a na Legas ya bukaci tsawaita umarnin taƙaita wuraren zanga-zangar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos - Babbar kotun jihar Legas mai zama a Igbosere ta ƙara yanke hukunci kan wuraren da ya halatta matasa su yi zanga-zangar da suka fara a jihar.

Kotun ta tsawaita wa'adin umarnin da ta bayar a baya na taƙaita zanga-zangar matasan a wurare biyu, filin shaƙatawa na Freedom da filin shakatawa na Peace.

Kara karanta wannan

An ga bidiyo ta koma talla, jama'a sun kawowa tsohuwar malamar makaranta tallafi

Matasa a wurin zanga-zanga.
Kotu ta tsawaita umarnin hana zanga zanga sai a wuri 2 a jihar Legas Hoto: Contributor
Asali: Twitter

Mai shari'a S.I. Sonaike ce ta yanke wannan hukuncin a buƙatar da Antoni Janar kuma kwmaishinan shari'a na Legas, Lawal Pedro, SAN, ya shigar ta neman tsawaita umarnin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnatin Legas ta nemi tsawaita dokar

Kamar yadda Leadership ta ruwaito, daraktan sashin shari'a, Hameed Oyenuga, shi ne ya wakilci kwamishinan shari'a na jihar Legas a zaman kotu yau Talata.

Ya shaidawa alkalin kotun cewa tuni aka kai takardar sammacin karar ga duka waɗanda ake ƙara a shari'ar watau wakilan masu zanga zanga.

A cewarsa, duk da cewa wadanda ake kara ba su amsa ba har yanzu, amma akwai bukatar a tsawaita dokar taƙaita zanga-zangar zuwa wurare biyu.

Wane hukunci kotu ta yanke a Legas?

Da take yanke hukuncu, mai shari'a Sonaike ta bayyana gamsuwarta bisa yadda Antoni Janar ya bi umarnin da mai shari'a Ogundare ya bayar tun farko, Channels tv ta rahoto.

Kara karanta wannan

Zanga zanga ta ƙara ɗaukar zafi, matasa sun tafka ɓarna a hedkwatar jam'iyyar APC

Sannan ta ba da umarnin a takaita zanga-zangar a wuraren shakatawa na Fredom da na Peace da ke a yankunan Ojota da Ketu na jihar har sai an cika umarnin farko.

Masu zanga-zanga sun ɗauki hutu

A wani rahoton kuma jagororin da suka shirya zanga-zanga a jihar Legas sun sanar da janyewa domin duba ci gaba da suka samu tun da aka fara zuwa yau.

Kwamared Hassan Taiwo Soweto, ɗaya daga cikin jagororin zanga-zanga ya ce ba za su ji tsoron barazanar hukumomin tsaro ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262