Zanga Zanga: An Kama Mutumin da Ke Ɗinka Tutocin Ƙasar Rasha a Jihar Kano

Zanga Zanga: An Kama Mutumin da Ke Ɗinka Tutocin Ƙasar Rasha a Jihar Kano

  • Jami'an tsaro sun kama wani tela mai suna Ahmed bisa zarginsa da yaɗa tutocin ƙasar Rasha a jihar Kano a lokacin zanga-zanga
  • Rahotanni sun nuna matasa sun fara ɗaga tutocin ƙasar ketaren ne a makon da ya wuce, amma lamarin ya ƙara ƙamari a ranar Litinin
  • Shugaba Bola Tinubu dai ya gargaɗi masu zanga-zanga su dakata haka nan domin ba zai bari su ci ga a da tayar da yamutsi a kasa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Rahotanni sun nuna cewa an damƙe daya daga cikin mutanen da ke dinƙa tutocin kasar Rasha a birnin Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.

An tattaro cewa dubannin ƴan Najeriya da suka fita zanga-zangar kin jinin manufofin gwamnati mai ci sun fara ɗaga tutar ƙasar Rasha a jihohi daban-daban.

Kara karanta wannan

Kasar Rasha ta yi magana kan masu zanga zangar da ke ɗaga tutocinta a Najeriya

Yan sanda sun kama tela a Kano.
Zanga zanga: Wanda ake zargi da ɗinka tutocin ƙasar Rasha ya shiga hannu a Kano Hoto
Asali: Twitter

Daily Trust ta ce lamarin dai ya faru ne a makon da ya gabata a wurare ƙalilan, amma zuwa yau Litinin adadin wadanda ke daga tutoci ya karu sosai.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya gargaɗi masu zanga-zanga

Hakan na zuwa ne bayan shugaban ƙasa Bola Tinubu ya gargadi masu zanga-zangar da kada su bari a yi amfani da su wajen yada wata manufa da ta sabawa doka.

Shugaba Tinubu ya ce:

"Yanzu da muka shafe shekaru 25 muna shan romon mulkin dimokuradiyya, kada ku bari makiya su yi amfani da ku wajen tallata manufar da ta saɓawa tsarin ƙasarmu, da za ta mayar da mu baya."

Tutar Rasha: An kama tela a Kano

Sai dai a yau Litinin, dakarun ƴan sanda suka cafke wani tela da ke ɗinka tutocin rasha tare da wasu matasa da ke ɗaga tutocin a wurin zanga-zanga.

Kara karanta wannan

Ministan Buhari ya mayar da martani ga Bola Tinubu, ya goyi bayan zanga zanga

Bayanai sun nuna cewa an kama telan mai suna Ahmed Bello ɗauke da wasu tutocin ƙasar Rasha da yawa a hannunsa a Kano.

Tuni dai ƴan sanda suka sakaya shi a bayan kanta domin ci gaba da bincike kan lamarin, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Tinubu ya gana da hafsoshin tsaro

A wani rahoton kuma Bola Ahmed Tinubu ya shiga ganawa da hafsoshin tsaro a fadar shugaban ƙasa da ke babban birnin tarayya Abuja ana tsaka da zanga-zanga.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima da shugaban ma'aikatan fadar gwamnati, Femi Gbajabiamila sun halarci taron yau Litinin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: