Nasir El-Rufa'i: An Haifa Wa Gwamnan APC Dan Shekara 63 Ya Mace, Hotuna Sun Fito

Nasir El-Rufa'i: An Haifa Wa Gwamnan APC Dan Shekara 63 Ya Mace, Hotuna Sun Fito

  • Matar gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai ta haifa masa santaleliyar budurwa, wacce itace ta huɗu da su ka haifa a tare da ita
  • Hotunan El-Rufai da matarsa Aisha Ummi Garba El-Rufai da kuma jaririyar sun karaɗe Intanet biyo bayan ɗora su da babban ɗansa ya yi a ranar Laraba, 10 watan Mayu
  • Babban ɗan El-Rufai, wato Bello El-Rufai ya nuna godiya ga Ubangiji sannan kuma ya bayyana sunan jaririyar da Fatima Layan

Matar Nasiru El-Rufai, gwamnan jihar Kaduna, Hajiya Aisha Ummi Garba El-Rufai ta haifo musu santaleliyar 'ya mace, wacce ita ce ɗiya ta huɗu da su ka haifa da gwamnan.

Daily Trust ta ce an raɗawa jaririyar suna Fatima Layan El-Rufai kamar dai yadda babban ɗan El-Rufai wato Bello El-Rufai ya sanar.

El-Rufai and Family
Hotunan Matar Gwamnan Kaduna, Hajiya Aisha Ummi Garba, El-Rufai, Bello El-Rufai. Hoto: City Scoop NG
Source: UGC

A ranar Laraba, 10 ga watan Mayu ne dai Bello El-Rufai ya bayyana labarin gami da ɗora hotunan a soshiyal midiya kamar yadda PM News ma ta wallafa.

Kara karanta wannan

El-Rufai: Ba Zan Riƙa Zuwa Kaduna Ba Sai In Ta Kama Bayan Kammala Wa'adina

Kamar dai yadda ya rubuta a shafinsa:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“Tare da tsatson El-Rufai na baya-bayan nan, muna farin ciki da samun ki antin mu.”

El-Rufai ya magantu kan muƙamin ministan Abuja ƙarƙashin Tinubu

Gwamnan na jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai ya bayyana cewa ba ya muradin riƙe kujerar ministan birnin tarayya ƙarƙashin zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu.

El-Rufai, wanda yanzu haka dai ya ke da shekaru 63 a duniya, ya taɓa riƙe muƙamin ministan birnin tarayya a ƙarƙashin tsohon shugaban ƙasar Najeriya, Olusegun Obasanjo, daga 13 ga watan Yuli na shekarar 2003, zuwa 27 ga watan Yuli na shekara ta 2007.

El-Rufai ya sha yabo sannan kuma ya yi suna sosai a wannan muƙami da ya riƙe na ministan birnin tarayya wanda a lokacin ya yi aiki tuƙuru wajen zamanantar da birnin na tarayya.

Da gaske ne Tinubu zai baiwa El-Rufai shugaban ma'aikata? El-Rufai ya yi bayani

Kara karanta wannan

Kafin Ya Shilla Turai, Tinubu Ya Yi Kus-Kus Da Zabin APC a Shugabancin Majalisar Wakilai, Bayanai Sun Bayyana

Nasiru El-Rufai ya musanta jita-jitar da ke yawo kan cewar ya na kuma neman muƙamin shugaban ma'aikata a gwamnatin Tinubu.

Ya ce ba wai dole sai mutum ya na cikin gwamnati ba ne zai iya bayar da gudummawarsa wajen kawo ci gaba. El-Rufai ya ƙara jaddada irin jajircewarsa wajen ganin nasarar gwamnatin Tinubu.

El-Rufai ya kuma bayyana cewa ya na da buƙatar ya ɗan huta bayan kammala wa'adinsa na gwamna, duk da dai ya ce a shirye ya ke ya riƙa bada shawarwari wajen ci gaban ƙasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng