Tsohon Dan Majalisar Dokokin Jihar Oyo Okunola Ya Mutu Bayan Ya Yi Fama Da Rashin Lafiya

Tsohon Dan Majalisar Dokokin Jihar Oyo Okunola Ya Mutu Bayan Ya Yi Fama Da Rashin Lafiya

  • Tsohon dan majalisar dokokin jihar Oyo, Tirimisiyu Okunola, ya kwanta dama
  • Dan uwan marigayin, Bashir Okunola, ya bayyana cewa yayan nasa ya mutu ne sakamakon ciwon siga
  • Okunola wanda ke jin radadin mutuwar dan uwan nasa ya tabbatar da da lamarin a wata wallafa da ya yi a shafinsa na Facebook

Allah ya yi wa tsohon dan majalisar dokokin jihar Oyo, Tirimisiyu Okunola, rasuwa.

Jaridar The Punch ta rahoto cewa kanin marigayin, Bashir Okunola ne ya sanar da labarin mutuwar tsohon dan majalisar a ranar Lahadi, 5 ga watan Maris, 2023 a shafinsa na Facebook.

Marigayi tsohon dan majalisa Tirimisiyu Okunola
Tsohon Dan Majalisar Dokoki Daga Jihar Oyo Okunola Ya Mutu Hoto: Tirimisiyu Okunola
Asali: Facebook

Abun da ya yi sanadiyar mutuwar Okunola

Okunola ya wakilci mazabar Ido na jihar tsakanin 2007 da 2011 karkashin inuwar jam'iyyar All Nigeria People’s Party (ANPP), sannan daga baya ya sauya sheka zuwa Peoples Democratic Party (PDP).

Kara karanta wannan

Shugaba Buhari Ya Mika Ta'aziyya Ga Iyalan Sani Abacha Kan Rashin Dansu

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

An tattaro cewa marigayin ya mutu ne sakamakon lalurar ciwon siga.

Da yake martani kan lamarin, kanin marigayin ya je shafinsa na Facebook inda ya tabbatar da mutuwar dan siyasar.

Ya rubuta a shafinsa:

“Haaaaa yaya me yasa ka tafi ka barmu kwatsam Hon. Tirimisiyu Olasupo Okunola.

Dan marigayi Sani Abacha ya kwanta dama

A wani labarin kuma, mun ji cewa Allah ya karbi ran Abdullahi Abacha, daya daga cikin 'ya'yan marigayi shugaban kasa a mulkin soja, Janar Sani Abacha.

Marigayi Abdullahi mai shekaru 34 a duniya ya amsa kiran mahaliccinsa a ranar Asabar, 4 ga watan Maris a cikin barcinsa, kamar yadda yayarsa, Gumsu Sani Abacha ta wallafa a shafinta na Twitter.

Tuni aka yi jana'izarsa a makabartar Gudu da ke babban birnin tarayya Abuja bayan an sallaci gawarsa a babban masallacin Juma'a na Abuja.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Hawaye, Alhini Yayin Da Dan Marigayi Sani Abacha Ya Rasu A Abuja

Shugaba Buhari ya mika ta'aziyyarsa ga iyalan Sani Abacha kan mutuwar dansu

Har ila yau, shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Asabar, 4 ga watan Maris, ya mika sakon gaisuwar ta'aziyya ga Hajiya Maryam Sani Abacha a kan babban rashi da ta yi na danta.

Da yake addu'an Allah ya ji kan matashin, shugaban kasar a wata sanarwa daga kakakinsa, Mallam Garba Shehu ya roki Allah da ya baiwa iyalan marigayi Abacha juriyar wannan rashi da suka yi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Tags: