Yanzu-yanzu: Kotu a birnin Landan ta hana Ike Ekweremadu beli, tace a garkameshi a Kurkuku

Yanzu-yanzu: Kotu a birnin Landan ta hana Ike Ekweremadu beli, tace a garkameshi a Kurkuku

Landan - Kotun kasar Birtaniya dake Landan ta hana tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ike Ekweremadu da matarsa Beatrice, beli.

Kotun ta bada umurnin a garkamesu a magarkama, rahoton AriseNews.

Ike Ekweremadu tare da matarsa sun gurfana yau Alhamis gaban kotun majistaren Uxbridge.

da dumi
Yanzu-yanzu: Kotu a birnin Landan ta hana Ike Ekweremadu beli, tace a garkameshi a Kurkuku
Asali: Original

An damke Sanata Ekweremadu da matarsa kan yunkurin satar sashen jikin wani yaro

Hukumomi a kasar Birtaniya ta damke tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Ike Ekweremadu, da matarsa Beatrice kan laifin kai wani yaro kasar don cire wani sashen jikinsa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hukumar yan sandan kasar ta tabbatar da labarin cewa an garkamesu a kurkuku kuma za'a gurfanar da su a kotu ranar Alhamis bayan gudanar da bincike, rahoton Skynews.

Kara karanta wannan

An hana matar Ekweremadu ganinsa yayin da yaransu suka bayyana a kotu

Yan sandan sun kara da cewa an kaddamar da bincike ne bayan sanar da su wasu sun kawo dan wani kasar kuma hakan ya sabawa dokar bautar zamani na Birtaniya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel