An samu ci gaba: Majalisa ta amince a kara yawan makarantun lauyoyi a kasar nan

An samu ci gaba: Majalisa ta amince a kara yawan makarantun lauyoyi a kasar nan

  • Majalisar dattajai a Najeriya ta amince a sake kafa wasu cibiyoyi na ilimin lauya a fadin kasar nan
  • Majalisar ta amince da kafa makarantun a shiyyoyi shida na kasar nan kamar yadda rahotanni suka bayyana
  • A baya kasar na da makamantun lauyoyi shida, yanzu an samu karin bakwai bayan amincewar majalisar

FCT, Abuja - Majalisar dattijai a ranar Talata 8 ga watan Fabrairu ta zartas da wani kudiri na kafa karin makarantun lauyoyi a shiyyoyin kasar nan shida, Daily Trust ta ruwaito.

Hakan ya biyo bayan nazarin rahoton kwamitin majalisar dattijai mai kula da harkokin shari’a, ‘yancin dan Adam da kuma harkokin doka, wanda Sanata Opeyemi Bamidele (APC, Ekiti) ya jagoranta.

Majalisa ta amince da kafa makarantun lauyoyi a fadin kasar ban
An samu ci gaba: Majalisa ta amince a kara yawan makarantun lauyoyi a kasar nan | Hoto: dailytrust.com
Source: UGC

Jerin Makarantun Lauyoyi da ake dasu

Kara karanta wannan

Buhari: Ci Gaban Najeriya Ya Dogara Ne Ga Kimiyya Da Fasaha

Rahoton The Nation ya kawo adadin makarantun da ake dasu kafin a amince da karin. Makarantun lauyoyi da ake da su a yanzu sune kamar haka:

  1. Legas (Kudu maso Yamma)
  2. Abuja (Arewa ta Tsakiya)
  3. Yola (Arewa maso Gabas)
  4. Kano (Arewa maso Yamma)
  5. Enugu (Kudu maso Gabas)
  6. Yenegoa (Kudu maso Kudu)

Karin makarantu 7 da za a kafa

Karin cibiyoyin da majalisar ta amince da su sun hada da:

  1. Makarantar Lauyoyi ta Kogi (Arewa ta Tsakiya)
  2. Makarantar Lauyoyi ta Maiduguri, Borno (Arewa maso Gabas)
  3. Makarantar Lauyoyi ta Argungu, Kebbi (Arewa maso Yamma)
  4. Makarantar Lauyoyi ta Okija, Anambra (Kudu maso Gabas)
  5. Makarantar Lauyoyi ta Orogun, Delta (Kudu maso Kudu)
  6. Makarantar Lauyoyi ta Ilawe, Ekiti (Kudu maso Yamma)
  7. Makarantar Lauyoyi ta Jos, Filato (Arewa Ta Tsakiya)

Majalisa ta tabbatar da Farfesa Ayo Omotayo a matsayin sabon shugaban NIPSS

Kara karanta wannan

Jerin matsaloli 6 da Kwankwaso yake bukatar ya tsallake kafin ya shiga Aso Rock a 2023

A wani labarin, Majalisar Dattawar Najeriya ta tabbatar da Farfesa Ayo. O. Omotayo a matsayin Direkta Janar ta Cibiyar Koyar Ta Manyan Ma'aikata, NIPSS da ke Kuru, Jihar Plateau.

An samu wannan bayanin ne ta wata takarda wacce hadimin watsa labarai na musamman ga shugaban majalisar tarayya, Ezrel Tabiowo, a ranar Talata ya saki.

A cewar sanarwar, an tabbatar da Omotayo ne bayan an yi nazari kan rahoton kwamitocin Ayyukan Gwamnati da Daidaito wurin nadin mukami da ayyukan gwamnati.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng