‘Yan bindiga sun aika mutane 1, 192 barzahu, sun dauke 3, 348 cikin shekara 1 a Kaduna
- Alkaluman da gwamnatin jihar Kaduna ta fitar ya nuna ‘yan bindiga sun kashe mutane fiye da 1, 000
- Rahoton da aka fitar ya nuna an yi garkuwa da Bayin Allah fiye da 3, 000 a Kaduna a shekarar bara
- Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida ya bayyana wannan a wani rahoto da ya gabatar dazu
Kaduna - Akalla mutane 1, 192 suka mutu a hannun ‘yan bindiga, sannan kuma an yi garkuwa da wasu mutum 3, 348 a jihar Kaduna a shekarar da ta wuce.
Jaridar Daily Trust ta ce gwamnatin jihar Kaduna ta fitar da wadannan alkaluma a makon nan.
Wannan bayani yana cikin rahoton harkar tsaro da aka fitar daga watan Junairu zuwa Disamban 2021 wanda kwamishinan tsaron cikin gida ya gabatar dazu.

Kara karanta wannan
Nasara: 'Yan sanda sun halaka 'yan ta'adda 23, sun yi ram da 'yan bindiga 37 a Sokoto
Mista Samuel Aruwan ya gabatar da wannan rahoto ne ga Mai girma gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai a ranar Talata, 1 ga watan Fubrairu 2022.
Samuel Aruwan ya ce an samu mutuwar mutane 720 a yankin tsakiyar Kaduna a sakamakon garkuwa da mutane, rikicin kabilanci, da sauran tashin-tashina.
Blueprint ta ce wadanda aka kashe sun hada da maza 1, 038, mata 104 da kananan yara 50. Alkaluman sun nuna an samu karuwar mace-mace da sata a bana.

Asali: Twitter
Har ila yau an tabbatar da satar shanu 10, 261 a shekarar baran, adadin satar da aka yi ya nunku.
Kwamishinan yake cewa an samu mace-mace har 406 a sakamakon rikicin garuruwa da satar mutane a yankin kudancin jihar Kaduna a shekarar da ta wuce.
Kiran Mai girma Nasir El-Rufai
Gwamna Nasir El-Rufai ya ce alkaluman da aka fitar sun nuna cewa kusan a kullum sai ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane tara a jihar Kaduna a shekarar 2021.
El-Rufai ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta samar da sansanin sojoji a Arewa maso yamma makamancin wanda aka kafa domin yakar ‘yan Boko Haram.
“Kirkirar irin wannan sansani zai bada dama a bullowa sha’anin yakar rashin tsaro gada-gadan a jihohi shida da abin ya shafa.”
“Wannan zai taimakawa sojoji, ‘yan sanda, dakarun SS, ‘yan banga da sauran ‘yan sa-kai wajen yakar masu tada kafar-baya.”
- Malam Nasir El-Rufai
Hari a Zangon Kataf
A ranar Litinin ne aka ji cewa miyagun ‘Yan bindiga sun kuma shiga yankin Kurmin Masara a karamar hukumar Zangon-Kataf, a jihar Kaduna sun yi ta'adi.
Wannan ne hari na biyu da ‘Yan bindiga suka kai a kauyen a cikin kwanaki biyu da suka wuce.
Asali: Legit.ng