Shugaba Bola Tinubu ya yi hasashe cewa farashin kayan abinci zai sauka ƙasa da kashi 10 a 2026, yana nufin inganta rayuwa da bunƙasar tattalin arzikin Najeriya.
Shugaba Bola Tinubu ya yi hasashe cewa farashin kayan abinci zai sauka ƙasa da kashi 10 a 2026, yana nufin inganta rayuwa da bunƙasar tattalin arzikin Najeriya.
Bankin CBN ya fitar da hasashe game da yadda farashin man fetur zai kasance a Najeriya a 2026 lura da alkaluman tattalin arziki. Ya ce lita za ta kai N950 a 2026.
Majalisar Dokokin Legas ta amince da kasafin kuɗin Naira tiriliyan 4.44 na 2026 don ayyukan raya ƙasa, lafiya, da ilimi ƙarƙashin tsarin T.H.E.M.E.S+.
Babbar Kotun Tarayya ba ta shirya sake duba hukuncin Nnamdi Kanu ba, binciken CableCheck ya tabbatar da rashin hujja. Lauyan Kanu ya bayyana wannan a matsayin ƙarya.
Sanata Basiru ya nemi Nyesom Wike ya yi murabus, yayin da magoya bayan APC suka yi zanga-zanga a Abuja suna neman Shugaba Tinubu ya kori Ministan na FCT nan take.
Kungiyar NADECO USA ta roki Shugaba Tinubu ya sallami Ministan Abuja, Nyesom Wike, don kawo ƙarshen rikicin siyasa a Jihar Rivers kafin zaɓen 2027.
Rundunar 'yan sanda reshen jihar Benuwai ta tabbatar da hallaka wani kasurgumin 'dan bindiga da ya addabi jama'a a wasu yankuna mai suna, Terkaa Samuel.
Farashin kilogram daya na iskar gas din girki ya sauka zuwa N1,000 - N1,400 yayin da gas din ya wadata a Legas da sauran jihohi bayan janye yajin aikin ma'aikata.
Rahotanni sun tabbatar da rasuwar Sarkin Kagarko a jihar Kaduna, Alhaji Sa’ad Abubakar, bayan fama da jinya, inda ya rasu a yau Alhamis 8 ga watan Janairun 2026.
Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa, Janar Tukur Buratai mai ritaya, ya shigar da ƙara ta Naira biliyan daya kan Danjuma Ali-Keffi, bisa zarginsa da faɗa da bata suna.
Labarai
Samu kari