Latest
Rundunar ƴan sanda a jihar Taraba ta cafke wasu jami’an hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) tare da kwato kayayyakin zaɓe da ake zargin sun karkatar.
Am samu mummunar ambalihar ruwa a jihar Kebbi wadda ta lalata gidaje da gonaki. Gwamnatin Kebbi ta ba da tallafi ga mutanen da lamarin ya ritsa da au.
Yayin da za a shafe kwanaki 3 ana sheka ruwan sama a Arewacin Najeriya, NiMet ta ce za a samu ambaliya a Kebbi, Gombe da Bauchi da wasu jihohin Arewa ta Tsakiya.
Hukumar zaben mai zaman kanta, INEC ta bayyana zaben majalisar dokoki a Kaura Namoda ta Kudu a Zamfara wanda bai kammalu ba saboda soke wasu rumfunan zabe.
Jam'iyyar APGA mai mulki a jihar Anambra ta samu nasara a zaben cike gurbi na kujerar sanatan Anambra ta Kudu. Dan takarar APGA ya lallasa abokan hamayyarsa.
Jam'iyyar NNPP da APC sun lashe zabukan cike gurbi a Kano, inda kowacce jam’iyya ta dauki kujeru daya, yayin da APC ta koka, NNPP ta ce an yi gaskiya a zaben.
Mai ba shugaban kasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa an kama manyan shugabannin kungiyar Ansaru da suka jagoranci harin gidan yarin Kuje.
An ayyana dan takarar jam’iyyar APC, Felix Joseph Bagudu a matsayin wanda ya lashe zaben cike gurbin kujerar majalisar wakilai na Chikun–Kajuru a jihar Kaduna.
Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta samu nasara a zaben cike gurbi da aka gudanar na kujerar dan majalisar wakilai mai wakiltar Garki/Babura.
Masu zafi
Samu kari