Bayan Gama Zagayen Farko, An Bayyana Bukata 1 da Amurka Ta Amince Za Ta Yi Wa Iran

Bayan Gama Zagayen Farko, An Bayyana Bukata 1 da Amurka Ta Amince Za Ta Yi Wa Iran

  • Amurka ta amince ta saki wasu kadarorin kasar Iran, lamarin da ya kara karfafa gwiwar kasar wajen ci gaba da tattaunawa a Pakistan
  • Wata majiya da ke kusa da tawagar Iran a Islamabad ta ce Amurka ta kuma amince za ta umarci Isra'ila ta rage hare-hare a Lebanon
  • Bayanai sun nuna cewa an kammala zagayen farko na tattaunawa, wacce aka kira da mafi sirri idan aka kwatanta da na baya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Iran - Rahotanni daga tawagar Iran sun bayyana cewa kasar Musulunci ta amince ta koma teburin tattaunawar sulhu ne bayan Amurka ta yarda ta saki wasu kadarorin Iran da aka rike.

Wannan na daga cikin muhimman bukatun da Iran ta gabatar a cikin sharudda 10 da ta shimfida gabanin tsagaita wuta a yakin Gabas ta Tsakiya.

Kara karanta wannan

An kammala tattaunawa ta farko, an ji yadda ta kaya tsakanin Amurka da Iran

Shugaba Trump.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump Hoto: Joe Riddle
Source: Getty Images

Sai dai har yanzu Amurka ba ta tabbatar da wannan mataki a hukumance ba, kamar yadda tashar Al-Jazeera ta ruwaito.

Rage hare-hare a Lebanon

Rahotanni sun kuma nuna cewa bayan haka, Iran ta samu wani irin tabbaci daga Amurka cewa Isra’ila za ta rage kai hare-hare a Lebanon.

Haka kuma wasu kafofin yada labarai na Iran sun ruwaito cewa Amurka za ta saki kudaden Iran da aka rike.

Sai dai babu wani tabbaci daga bangaren Amurka ko Isra’ila dangane da wannan batu, duk da cewa an samu raguwar hare-hare a Beirut da yankunan kudancin Lebanon.

Iran na tsaka mai wuya kan Lebanon

A halin yanzu, Iran na cikin wani yanayi mai sarkakiya, inda a bangare guda, ba ta son gaza kare kanta ko kuma alakarta da kungiyar Hezbollah ta Lebanon ba, domin hakan na da alaka da martabarta da tasirinta a yankin.

A bangare guda kuma, ba ta son rusa yarjejeniyar tsagaita wuta saboda wasu dalilai na waje, lamarin da ke kara jefa Iran cikin yanayi mai cike sarkakiya.

Kara karanta wannan

Sabon shirin yaki: Amurka ta fadi manyan makaman da ta zargi China za ta ba Iran

Bayanai sun nuna cewa an kammala zagayen farko na tattaunawa, wacce aka kira da mafi sirri idan aka kwatanta da na baya, saboda karancin bayanan da ke fita zuwa jama’a.

Islamabad.
Harabar wurin tattaunawar Amurka da Iran a birnin Islamabad Hoto: Pool
Source: Getty Images

Amurka da Iran sun ci gaba da tattaunawa

A halin yanzu, ana ci gaba da tattaunawa a otel din Serena da ke Islamabad, inda aka ruwaito cewa wakilan sun sake komawa wani zagaye domin ci gaba da tattaunawa a cikin dare.

Lokacin da aka tattara wannan rahoto, karfe 11 na dare ne a Islamabad, kuma babu alamar cewa bangarorin za su tashi daga tattaunawar nan ba da jimawa ba.

A wani labarin, kun ji cewa

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: