Bayan Ta Sha Alwashin Kashe Netanyahu, Iran Ta Kai Farmaki Muhimman Cibiyoyi 2 a Isra'ila

Bayan Ta Sha Alwashin Kashe Netanyahu, Iran Ta Kai Farmaki Muhimman Cibiyoyi 2 a Isra'ila

  • Dakarun sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran sun ci gaba da kai hare-hare kan muhimman wurare a kasar Isra'ila
  • A wata sanarwa da suka fitar yau Asabar, 15 ga watan Maris, 2026, sojojin Iran sun ce sun harba makamai zuwa wasu cibiyoyin tsaron kasar ta Yahudawa
  • Haka zalika wasu rahotanni sun nuna cewa Iran ta jikkata akalla mutane biyu a sababbin hare-haren da ta kai Isra'ila da safiyar yau

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Israel - Dakarun sojojin Iran sun sanar da ci gaba da kai hare-hare da makamai masu linzami kan muhimman wurare a kasar Yahudawa watau Isra'ila.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna shakku kan halin da Firaministan Isra'ila ke ciki, wanda Iran ta sha alwashin cewa za ta faraute kuma ta tura shi lahira.

Kara karanta wannan

Abin da Iran ta ce kan ganin bayan Netanyahu yayin da ake rade radin ya mutu

Makami.
Yadda ake musayar wuta da makamai masu linzami a Gabas ta Tsakiya Hoto: Anadolu
Source: Getty Images

Iran ta kai hari cibiyoyin tsaron Isra'ila

Tashar Al-Jazeera ta ruwaito cewa a wata sanarwa da sojojin Iran suka fitar yau Asabar, sun ce sun kai hare-hare da jirage marasa matuka kan muhimman cibiyoyin tsaron Isra'ila.

Sanarwar ta ce hare-haren sun nufi hedikwatar rundunar ‘yan sanda ta Lahav 433 ta Isra'ila da kuma cibiyar sadarwar tauraron ɗan adam ta tsaro ta Gilat Satellite Communications Center.

Sai dai sojojin Iran ba su bayyana takamaiman biranen da suka kai hare-haren ba, haka kuma ba su fadi irin barnar da aka yi ba.

Rahoton jikkata mutane a Isra’ila

A gefe guda kuma, rahotanni daga Isra’ila sun ce mutane biyu masu shekaru kusan 50 sun samu ƙananan raunuka bayan wani sabon harin makamai masu linzami daga Iran.

Hukumar agajin gaggawa ta Isra’ila 'Magen David Adom' ta ce an jikkata mutanen ne sakamakon fashewar wani makami da ya fado yankinsu.

Kara karanta wannan

To fa: Musayar wutar da ake tsakanin Amurka, Isra'ila da Iran ta shiga wani muhimmin mataki

The Times of Israel ta ruwaito cewa wani makami mai linzami da ke ɗauke da kananan bama-bamai ya tarwatse a birnin Eilat da ke kudancin Isra’ila da wasu sassan ƙasar

Hukumomin Eilat sun ce an harbo wannan makami tun kafin ya kai ga birnin ta hanyar tsarin kariyar sararin samaniya na Isra’ila.

Jagoran Iran.
Jagoran Iran, Mojtaba Khamenei na jagorantar maida martani a yakin kasarsa da Amurka da Isra'ila Hoto: Anadolu
Source: Getty Images

Haka zalika wasu rahotanni sun ce wasu makaman rokoki sun faɗa a cikin biranen: Bnei Brak da Ramat Gan, wadanda ke cikin babban yankin Tel Aviv.

‘Yan sandan Isra’ila sun ce suna binciken wurare da dama inda tarkacen makamai da rokoki suka faɗi.

Iran ta shirya koyawa Amurka darasi

A wani labarin, kun ji cewa gwamnatin kasar Iran ta sake jaddada shirinta na ci gaba da mayar da martani kan sansanonin sojojin Amurka da kasar Isra'ila.

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sha alwashin koya wa kassshen Amurka da Isra'ila darasin da ba za su taba mantawa da shi ba a tarihi.

Ma'aikatar harkokin wajen Iran ce ta bayyana hakan, tana mai cewa dakarun sojojin kasar ta Musulumci sun shirya tunkarar kowane irin kalubale a wannan yaki da ke gudana.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: