Fulani Makiyaya sun kai wata mumunan hari kauye

Fulani Makiyaya sun kai wata mumunan hari kauye

Wasu Fulani Makiyaya sun kashe kutane 3 ,sun jinkita 6 kuma sun banka ma kauye wuta a jihar Kaduna da kuma Fulanin makiyayan sun afka kauyen Godogodo.

Fulani Makiyaya sun kai wata mumunan hari kauye

Fulani makiyaya sun hallaka mutane 3 mazauna Dogon Daji da kuma Antang a godogodo ,karamar hukumar Jema’a a jihar Kaduna.

An kasance dai ana kai hari Godgodo ne tun watan yuli yayinda Fulani na ikirarin sun asalin mazauna wurin.

Wani mazauni kauyen yace: “ Da safen nan , wasu makiyaya suka kawo mana hari dogon daji. Sun kashe mutane 3 kuma sun kona wasu wurare sun raunata mutane.

Amma,mukaddashin shugaban karamar hokum jama’a. Mista Humble Katuka, yace an kashe mutane 2 a Antang kuma an kona gida 1 Antang.

Yace: “Labarin da samu yanzu na cewa an kashe mutane 2 a Dogon daji kuma an kona gidaje 2 a Atang. Sun kawar da hankalin soji da yan sandan da ke godgodo ne kafin sukayi wannan aika-aikan.

KU KARANTA: Wani dan bautan kasa ya mutu a Bayelsa

Amma jami’an tsaro sun gaggauto kuma zan je da kaina inga abinda ya faru.

Zaku tuna cewa an kai irin wannan hari a ranan asabar 2 ga watan satumba Godogodo inda aka kashe yan banga 4.

Jawabin da Kanal Sani Usman ya bada yace: “Rundunar division 1 a cikin wata harin da ta gudannar tare da yan sandan da yan banga a yau na wasu yan bindiga a Godogodo,a jihar Kaduna.

Jami’an tsaron sun kama wadannan mutanen : Lawal Gambo, Yau Sani, Bala Amodu, Ibrahim Maikaru, Abubakar Hassan da Bashiru Isa Ciroma. Amma , yan banga 4 sun rasa rayukansu kuma wasu 9 sun jinkata yayinda suke yunkurin kare harin da akayi domin asaran rayukan mutane da dukiyoyinsu.

Yanzu dai an kwantar da wutan kuma anan kokarin cimma wadanda suka arce a cikin yan barandan. Muna tabbatar wa jama’a cewa zamu kare rayuwarsu da dukiyoyinsu da kuma tabbatar da cewa an kama wadannan yan barandan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: