Hadiza Gabon da Adam Zango sun zama jakadu

Hadiza Gabon da Adam Zango sun zama jakadu

- Likkafar Hadiza Gabon da Adam A. Zango ta yi gaba

- Kamfanin taliyar 'yan yara ya nadasu jakadu

- Jaruman za su rika fitowa a duk tallace-tallacen kamfanin

Kamfanin taliyar ‘yan yara ta nada Hadiza Gabon da Adam A zango a matsayin jakadun samfurin taliyarta ta Indomie.

Hadiza Gabon da Adam Zango sun zama jakadu
Adam Zango da jami'an kamfanin a lokacin bikin sa hannu a yarjejeniyar aikin zama jakada, kamar yadda ya sa a shafinsa na Twitter

A cewar shafin kannywood.com na yanar gizo, wanda ya bayar da labarin, tare da sa hotunan jaruman biyu suna sa hannu a yarjejeniyar aiki ya ce, Hadiza da Adam sun samu sahalewar kamfanin taliyar ne na zama jakadunsa a tsawon shekara guda.

KU KARANTA KUMA: Shugaba Buhari yayi kira ga Nollywood

An dai yi bikin sa hannu a yajejeniyar aiki a tsakanin jaruman, da kuma kamfanin taliyar ne, wani gari da ba’a bayyana ba, a kuma hotunan da shafin ya yada, wasu manyan jami’an kamfanin taliyar ne su biyu, suka sa hannu a yarjejeniyar a madadin kamfanin, Hadiza da Adam kuwa, kowa ya sa hannu da kansa.

Hadiza Gabon da Adam Zango sun zama jakadu
Hadiza Gabon na sa hannu a takardar yarjejeniyar aikin da kamfanin a matsayin jakadiya, gefe kuma wakilan kamfanin ne.

Wannan jakadancin na nufin fitowa a tallace-tallacen kamfanin a kafofin yada labarai na rediyo, da gidajen Talbijin, da kuma manya-manyan allunan talla, baya ga wasu jerin abubuwa da kamfanin zai yi amfani da fuskokinsu a jiki don kiran kasuwa.

A baya dai, marigayiya Hafsatu Sharada wacce ake kira mai Aya, ta taba yiwa Kamfanin taliyar Jakadiya, a inda ta fito a tallacen-tallacen taliyarsa tare da ‘yan yara, wadanda aka rika sa wa a manya-manyan allunan talla da kuma gidajen Talbijin.

Fitowa a tallace-tallace na daya daga cikin manyan hanyoyin da jarumai a masana’antar shirya fina-finai ke samun babban tagomashi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng