Wani mumunan hadari ya faru a babban titin Lagos-Ibadan

Wani mumunan hadari ya faru a babban titin Lagos-Ibadan

–Wani hadari da ya faru a babban titin Lagos-Ibadan ya bar mutane 5 a mace

–Hakazalika mutane 15 ne suka samu rauni

–Wata mota Mazda tayi kicibis da Mitsubishi bayan an samu wani matsala

Wani mumunan hadari ya faru a babban titin Lagos-Ibadan
Hatsarin mota

Maza hudu da mace daya na aka bada rahoton cewa sun rasa rayukansu sakamakon wani mumunan hadari da ya faru a babban titin Lagos-Ibadan

Wasu mutane 15 kuma sun ji rauni a hadarin da ya faru a misalin karfe 4 na yamma a Ogunmakin,kusa gidan man Total.

Majiya ta bayyana cewa motocin da suka samu hadari su ne Mazda mai lamba KSF477XK da kuma wata mota Mitsubishi mai lamba MUS639DK. An tattara cewan hadarin ya jawo an tare hanyan wucewan mutane. Sai da jami’an hukumar tabbatar da tsaron hanya na jihar Ogun  suka dauke motocin a hanya.

KU KARANTA:Anyi shirin jibge sojoji 10,000 a Neja Delta

Yayinda kwamandan FRSC ,Ayobami Omiyale ya tabbatar da cewa mutane 20 ne abin ya shafa. Ya kara da cewa an kai wadanda suka ji rauni asibitin Ife-Oluwa da Ibadan Centre Hospital.

Ya bayyana cewan direbobin ne ummul khaba’isin hadarin saboda rashin hakuri. “ Muna baiwa direbobi shawaran cewa su dinga hakuri kuma su daina wuce juna musamman a wurarenda aiki ke gudana.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: