Buhari ya kai ziyara jihar Osun

Buhari ya kai ziyara jihar Osun

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya fara gudanar da ziyarar aiki na kwanan daya a jihar Osun a ranar Alhamis, 1 ga watan Satumba.

Jam’iyyar All Progressive Congress (APC) ta yada bidiyon isar sa jihar a shafinta na Twitter.

Jirgi mai saukar ungulun Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauka a makarantar kimiyya na Ataoja, Osogbo, inda Gwamnan jihar, Ogbeni Rauf Aregbesola ya jagoranci sauran manyan gwamnati domin su tarbi shugaban kasar.

KU KARANTA KUMA: An zargi Buhari da daukar nauyin harin makiyaya

Shugaban kasar Najeriya zai kaddamar da kyautar abincin gwamnatin tarayya ga shirin daluban  makarantar Firamare da kuma da kuma kaddamar da makarantar gwamnati na Osogbo. Za’ayi taron ne a harabar makarantar.

Buhari ne shugaban kasa na farko da ya kaddamar da aiki a jihar Osun.

Buhari ya kai ziyara jihar Osun
Buhari ya kai ziyara jihar Osun
Buhari ya kai ziyara jihar Osun

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng