An zargi Buhari da daukar nauyin harin makiyaya

An zargi Buhari da daukar nauyin harin makiyaya

-Mambobin Kungiyar Civil Liberties Organisation (CLO) sun zargi Shugaban kasa Muhammadu Buhari da sanya hannu a cikin hare-haren da Fulani makiyaya suka kai jihar Ekiti

-Kungiyar sun bayyana bacin ransu kan rashin kama su bayan kisan kiyashin da makiyaya sukayi ga yan unguwa 13 a Nimbo a ranar 25 ga watan Afrilu

An zargi Buhari da daukar nauyin harin makiyaya
Fulani makiyayi dauke da bindiga

Haushin cewa gwamnati bata sanya baki gurin maganin rikicin Fulani makiyaya a jihar Ekiti ba, yasa kungiyar Civil Liberties Organization (CLO) sun yanke shawarar cewa sakachin da  shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi yana iya yiwuwa yana da hannu a cikin hare-haren koma killa shi ke daukar nauyin su.

KU KARANTA KUMA: Gwamnatin tarayya ta kara kudin shigar motoci filin jiragen sama(Hoto)

Kungiyar ta jadadda cewa abu irin wannan yana faruwa a wata kasa a nahiyar Afrika, Turai ko wani bangare a duniya, da Buhari ya kasanace cikin mutane na farko da zasu fara sukar kashe- kashen amma yana yi kamar babu abunda ke faruwa a kasar sa.

har ila yau, kungiyar CLO sun nace a kan lura da kamu da kuma hukunta Ibrahim Adamumale, 20, wani Fulani makiyayi da ake zargi, an kama a Affa, karamar hukumar Udi dake jihar Enugu, da laifin samunsa da bindigar AK-47 tare da alburusai 24.

KU KARANTA KUMA: Wani matashi ya tashi bayan likitoci sun tabbatar da mutuwarsa (Hotuna)

Bayan haka, kungiyar sunyi Allah wadai da tserewar wasu yan kungiyar da aka kama kan zargin kisan kiyashi a Nimbo a ranar 25 ga watan Afrilu, inda aka kashe yan garin guda 13 duk da sahihanci a idanun fasaha.

Wandanda aka kama kan zargin harin Nimbo sune: Mohammed Zurai, Ciroma Musa, Sale Adamu, Suleiman Laute da kuma Haruna Laute.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng