Allah daya-gari bam-bam! Lefe hadda alade a wata kabila

Allah daya-gari bam-bam! Lefe hadda alade a wata kabila

Sanin kowa ne dai lefe wasu kaya ne da ake kaiwa gidan amarya a duk lokacin da zatayi aure. Ana kai lefe ne daga wurin miji kokuma dangin sa.

Kamar yadda Allah ya banbanta mu a kabilu-kabilu, haka ma kuma kowace kabila tana da irin nata salon na yin lefe dai-dai da al'adunta. A Najeriya wasu kabilu kamar na Kanuri dake a jihar Borno da kuma Ibo dake kudu maso-gabashin Najeriya sukan tsauwala yayin da iyalin mata kan bukaci abubuwa masu tarin yawa daga dangin miji a matsayin lefe wanda kuma wasu kabilun nasu babu tsada sosai.

A wani labari da aka wallaba a shafin sada zumunta na fesbuk na wani lefe da aka kai wa wata mai shirin zama amarya hadda alade a ciki. Kai ala dun ma bama daya ba ba biyu ba.

Allah daya-gari bam-bam! Lefe hadda alade a wata kabila

Sauran kayan lefen da aka kai sun hada da akuya baka, katan din kifi, buhunnan shinkafa da kuma kwalaben giya da dai sauran su.

Asali: Legit.ng

Online view pixel