Allah daya-gari bam-bam! Lefe hadda alade a wata kabila
Sanin kowa ne dai lefe wasu kaya ne da ake kaiwa gidan amarya a duk lokacin da zatayi aure. Ana kai lefe ne daga wurin miji kokuma dangin sa.
Kamar yadda Allah ya banbanta mu a kabilu-kabilu, haka ma kuma kowace kabila tana da irin nata salon na yin lefe dai-dai da al'adunta. A Najeriya wasu kabilu kamar na Kanuri dake a jihar Borno da kuma Ibo dake kudu maso-gabashin Najeriya sukan tsauwala yayin da iyalin mata kan bukaci abubuwa masu tarin yawa daga dangin miji a matsayin lefe wanda kuma wasu kabilun nasu babu tsada sosai.
A wani labari da aka wallaba a shafin sada zumunta na fesbuk na wani lefe da aka kai wa wata mai shirin zama amarya hadda alade a ciki. Kai ala dun ma bama daya ba ba biyu ba.
![Allah daya-gari bam-bam! Lefe hadda alade a wata kabila Allah daya-gari bam-bam! Lefe hadda alade a wata kabila](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt4st5lutp4fj.jpeg?v=1)
Sauran kayan lefen da aka kai sun hada da akuya baka, katan din kifi, buhunnan shinkafa da kuma kwalaben giya da dai sauran su.
Asali: Legit.ng