Dangote ya sauka daga jerin manyan masu kudi 100

Dangote ya sauka daga jerin manyan masu kudi 100

-Mai kudin Afrika, Aliko Dangote ya sauka daga jerin masu kudin duniya 100

-Dangote na da kimanin dala billiyan 15.4 (naira trilliyan 3.05) a watan Maris, yanzu ya koma Dala billiyan 11.1 (naira trilliyan 3.3) wanna ne dalilin da ya yasa ya kasance ya kudi a naira, amma ya talauce a Dala

Mai kudin Najeriya da Afrika, Alhaji Aliko Dangote ya sauka daga cikin jerin masu kudin duniya 100.

Dangote ya sauka daga jerin manyan masu kudi 100
Alhaji Aliko Dangote

Faduwar Dangote ya faru ne sakamakon faduwar naira.

A cewar Bloomberg, Alhaji Aliko Dangote wanda ya kasance mutun na 51 a masu kudin duniya a watan Maris na shekara 2016, ya sauka a yanzu zuwa lamba 101.

Kamfanin Dangote cement, daya daga cikin manyan hannun jarin Dangote a Najeriya, ya kasance kamfani mafi girma a kamfanin da ba mallakin gwamnati ba a Najeriya, kuma wanda suka fi samar da ciminti a yakin sahara Afrika.

A halin yanzu gidauniyar Dangote tayi alkawarin kuma gina hukumomin lafiya da mayakan Boko Haram suka lalata, musamman wadanda aka lalata a karamar hukumar Gujba da Gulani na jihar Yobe.

 KU KARANTA KUMA: labarai daga jaridun Najeriya

Dangote na da kimanin dala billiyan 15.4 (naira trilliyan 3.05) a watan Maris, yanzu ya koma Dala billiyan 11.1 (naira trilliyan 3.3) wanna ne dalilin da ya yasa ya kasance ya kudi a naira, amma ya talauce a Dala.

Duk da haka, Dangote yafi Donald Trump kudi, Billonoiyan Amurka kuma dan takarar shugabancin kasa, da kuma Oprah Winfey, mai gidan talabijin din US TV, ta biyu a cikin mata masu kudi a bakar fata na duniya. An kimanta cewa Trump da Oprah na da dala billiyan 4.5 da dala billiyan 3.1.

Kamfanin Dangote cement, daya daga cikin manyan hannun jarin Dangote a Najeriya, ya kasance kamfani mafi girma a kamfanin da ba mallakin gwamnati ba a Najeriya, kuma wanda suka fi samar da ciminti a yakin sahara Afrika.

A halin yanzu gidauniyar Dangote tayi alkawarin kuma gina hukumomin lafiya da mayakan Boko Haram suka lalata, musamman wadanda aka lalata a karamar hukumar Gujba da Gulani na jihar Yobe.

 

 

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng