Jonathan tare da iyalin sa a filin jirgin sama na Abuja (hotuna)

Jonathan tare da iyalin sa a filin jirgin sama na Abuja (hotuna)

An hangi Tsohon shugaban kasar Najeriya, Goodluck Jonathan, tare da matarsa Patience da dansu a filin jirgin sama na Abuja a ranar Lahadi 24 ga watan Yuli.

Jonathan tare da iyalin sa a filin jirgin sama na Abuja (hotuna)
Jonathan tare da iyalin sa a filin jirgin sama na Abuja (hotuna)
Jonathan tare da iyalin sa a filin jirgin sama na Abuja (hotuna)

Tsohon ministan harkokin sufurin sama, Osita Chidoka ne ya yada hotunan a shafin sadarwa na Twitter.

KU KARANTA KUMA: Kungiyoyin yan bindiga masu hatsari 5 daga Niger Delta

Mu tuna a makonni biyu da suka shige, Mr Jonathan wanda ya sauka a filin jirgin Port Harcourt international airport tare da matar sa, Dame Patience Jonathan sun samu tarba daga gwamnan jihar Rivers, Nyesome Wike da wasu jam’ian gwamnati.

Haka kuma, lokacin da Goodluck Ebele Jonathan baya kasar, jam’iyyar sa, Peoples Democratic Party (PDP) ta kasance cikin matsala kan wanda zai shugabanci jam’iyyar.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa wato Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) suna binciken yanda aka yi almubazaranci da dukiyan kasa, a na kuma binciken yan jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) wadanda ke da nasaba da abun.

A wata zantawa da jaridar Vanguard, Lawal ya nace kan cewa jam’iyyar PDP da ta kasance a kan mulki na tsawon shekaru 16, ya ba mambobin jam’iyyar dama a kan kudin kasa wanda wannan ne dalilin da ya sa a ke binciken cin hanci da rashawa a kansu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Tags: