Jihohin da rikicin addini ya afku a Najeriya

Jihohin da rikicin addini ya afku a Najeriya

-Jihohi bakwai da rikicin addini ka iya afkuwa

-Yan leken asiri sun ce Shugaban kasa Buhari kar ya dauki barazanar da wasa

Jihohin da rikicin addini ya afku a Najeriya

Nan da sannu rikicin addini mai tsanani na iya afkuwa a kasar Najeriya idan ba’a mayar da hankali ga rahotanni da yan leken asirin al’umman Najeriya ke kawo ba. A cewar wata majiya da jaridar Sahara Reporters ta samo, an motsa rikicin ne a siyasance, domin girgiza hadin kan kasa, ta hanyar farfado da kisan kiristoci da musulmai sukayi a arewa kwanaki.

Jihohin da aka lissafa sun hada da: Babban birnin tarayya, Abuja, jihar Niger, jihar Kaduna, Jihar Kano, Jihar Nasarawa, Jihar Plateau, da kuma jihar Benue. Majiyar sun kuma bayyana cewa yawan makamai da aka gano a muhimman unguwannin Abuja da sauran jihohi shiddan  ya isa dalili da zai sa gwamnatin tarayya karta dauki barazanar da wasa.

KU KARANTA KUMA: Harin makiyaya yafi karfin shugaba Buhari

An kuma samo rahoto cewa wadannan ne kashe-kashen addini da kabila da akayi amfani dashi gurin cimma wadannan yunkuri da ake shirin yi.

. Kisan da akayi a ranar 29 ga watan Mayu a jihar Niger na wani mutun mai shekaru 24 da jami’an tsaro uku;

. Kisan wata matar fasto a akayi a jihar Kano, a ranar 2 ga watan Yuni;

. Harin da aka kai wa wani mutun a Jihar Kaduna kan ya ci abinci a watan azumi; da kuma

. Kisan wata mace mai da’awar addinin kirista a Abuja, a ranar 9 ga watan Yuli. Wadan nan ne da hujjar da ake so ayi amfani da.

 

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng