Sanusi ya yi wa Hadimin El-Rufai mugun baki, ya bi shi saboda ya kira shi tsohon Sarki a taro

Sanusi ya yi wa Hadimin El-Rufai mugun baki, ya bi shi saboda ya kira shi tsohon Sarki a taro

  • Muhammadu Sanusi II ya ja kunnen Sani Dattijo a wajen taron KADIVEST6.0 a Kaduna
  • Tsohon Sarkin ya yi wa babban hadimin baki cewa shi ma zai sauka daga kan kujerarsa
  • Makonni da yin hakan ne aka sauke Dattijo daga shugaban Ma’aikatan gidan gwamnati

Kaduna - Khalifa Muhammad Sanusi II ya halarci wani taron kwadaito da masu hannun jari da gwamnatin jihar Kaduna ta shirya a watan Satumba.

A wajen wannan taro, shugaban ma’aikatan fadar gwamna, Muhammad Sani Dattijo ya yi jawabi, inda ya kira Muhammad Sanusi II da tsohon Sarkin Kano.

Mai martaba Sanusi II bai ji dadin yadda aka kira shi da tsohon Sarkin Kano ba, ya nuna sam babu wani abu mai kama da tsohon Sarki a sarautar gargajiya.

Kara karanta wannan

Shekara daya da rabi da Shugaba Buhari ya yi magana, har yau umarninsa bai fara aiki ba

Wannan ya sa Sarkin da aka tunbuke a 2019 ya gargadi Muhammad Sani Dattijo, har ya kira shi da tsohon shugaban ma’aikatan fadar gidan gwamnati.

Makonni kusan uku da yin wannan magana, sai ga shi Malam Muhammad Sani Dattijo ya rasa mukaminsa a wani sauyi da Gwamna El-Rufai ya yi jiya.

Malam Nasir El-Rufai ya bada sanarwar cire Dattijo daga kujerar da yake kai, kamar yadda amininsa, Khalifa Muhammadu Sanusi II ya yi hasashe.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Sanusi da El-Rufai
Sarki Sanusi da Gwamnan jihar Kaduna Hoto: dailytrust.com.ng
Asali: UGC

Abin da Sanusi II ya fada

“Da na saurari tsare-tsaren da kuma na ji maganar (Dattijo), zan kira shi tsohon shugaban ma’aikatan fadar gwamna, daga baya za ku fahimci dalili.”
“Nan gaba ka da ka kira ni tsohon Sarki, babu wani abu mai kama da haka.” – Sanusi II

Malam Muhammad Sani Dattijo

Mai girma gwamna El-Rufai ya maida Malam Dattijo a kan mukaminsa da ya bari a 2019. Dama can shi ne kwamishinan kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki.

Kara karanta wannan

Zargin batanci: Rikici ya barke tsakanin Sheikh AbdulJabbar Kabara da Lauyoyinsa a Zaman Kotu

Daga baya sai aka ji an nada matashin a matsayin sabon shugaban ma’aikatan gidan gwamnati. Dattijo, wanda ya na cikin manyan na hannun daman gwamna.

Daga baya sai aka ji an nada matashin a matsayin sabon shugaban ma’aikatan gidan gwamnati. Kafin 2015, Dattijo ya yi da shugaban majalisar dinkin Duniya.

2023: Hasashen Fasto Ayodele

Limamin INRI Evangelical Spiritual Church, Primate Ayodele ya ba Gwamnan Ebonyi, David Umahi shawara ya koma PDP, yace zai yi nadamar shiga APC.

An ji Ayodele yana cewa gwamna David Umahi da Ben Ayade za su gamu da takaici a 2023.. Faston yace sai Umahi ya yi da-na-sanin shiga APC a zaben 2023

Asali: Legit.ng

Online view pixel