Yanzu-yanzu: Yan Najeriya na korafin layukan MTN sun daina aiki a Abuja, da wasu jihohin Najeriya

Yanzu-yanzu: Yan Najeriya na korafin layukan MTN sun daina aiki a Abuja, da wasu jihohin Najeriya

Yan Najeriya sun yi korafi kan yadda layukan wayoyinsu na MTN suka daina aiki da yammacin ranar Lahadi, 9 ga watan Oktoba, 2021.

Mutane da dama daga birnin taraya sun bayyana cewa sun gaza kiran 'yan uwa da abokan arziki a waya.

Legit ta samu ji daga bakin wani ma'aikacin MTN wanda ya bukaci a sakaye sunansa, ya tabbatar da cewa akwai matsalar Network a fadin tarayya amma ana gyarawa.

A jawabin da kamfanin ya saki, ya tabbatar da cewa lallai akwai matsala amma ana kan gyara.

Yanzu-yanzu: Yan Najeriya na korafin layukan MTN sun daina aiki a Abuja, da wasu jihohin Najeriya
Yanzu-yanzu: Yan Najeriya na korafin layukan MTN sun daina aiki a Abuja, da wasu jihohin Najeriya
Asali: Original

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Hadimin Buhari kan sabbin kafafen yada labarai, Bashir Ahmad yace:

Kara karanta wannan

Ba a gama jimami kan samun matsala da Facebook ba, sai ga MTN sun shiga sahu

"Ba MTN dinka kadai ne baya aiki ba, kuma ba unguwarku kadai bace. yawancin masu amfani da MTN na fuskantar matsalar kira da ranan nan."

Wani mazaunin unguwar Lokogoma a Abuja, Usman, ya bayyana mana cewa:

"Na kasa kira ga layin MTN tun dazu."

Hakazalika wata dattijuwa mazauniyar Efab Estate dake Abuja tace:

"Shin layukan MTN na yi kuwa?"

Aisha Muhammad ta bayyana mana cewa:

"Ina ta kokarin kira mahaifiyata tun dazu amma abun ya gagara"

Abubakar Adamu yace:

Harda Manan jahar Niger

Kabir Hamisu Daura yace:

Har anan jihata ta katsina yanzu haka layi na baya tafiya yasa mini emergency

Auwalu Muhd Bashir Kurugu

"Harda Okene kogi state"

Asali: Legit.ng

Online view pixel