Zaben kananan hukumomin Kaduna: PDP ta lallasa APC a akwatin mazabar Gwamna El-Rufa'i

Zaben kananan hukumomin Kaduna: PDP ta lallasa APC a akwatin mazabar Gwamna El-Rufa'i

  • Gwamna El-Rufa'i ya rasa akwatin zabensa ga jam'iyyar PDP a zaben kananan hukumomi
  • Gwamnan ya kada kuri'arsa da safiyar Asabar a akwatin zaben
  • A cewar El-Rufa'i, ba dole bane jam'iyyarsa ta lashe kowani zabe ba

Kaduna - Jam'iyyar Peoples Democratic Party PDP ta lashe akwatin zabe kujerar shugaban karamar hukumar da kuma na kansila a mazabar gwamnan jihar, Nasir El-Rufa'i.

El-Rufa'i ya kada kuri'arsa da safe a akwatin mazabarsa dake Unguwar Sarki, karamar hukumar Kaduna ta Arewa, rahoton ChannelsTV.

Yayinda yake kada kuri'arsa, El-Rufa'i ya bayyana cewa bai zama dole jam'iyyarsa ta APC ta kashe zabe ba, kawai abinda yake bukata shine inganta zabe ta hanyar amfani da na'urar zamani.

A cewar gwamnan, kawo wannan na'urar ua nuna cewa gwamnatin APC a jihar Kaduna ba tada shirin magudin zabe.

Yayin sanar da sakamakon zaben, baturen zaben mazabar, Muhammad Sani, ya ce jam'iyyar APC ta samu kuri'u 62 a zaben shugaban karamar hukumar, yayinda PDP ta samu kuri'u 86.

A zaben Kansila kuwa, APC ta samu kuri'u 53 yayinda PDP ta samu kuri'u 100.

Yanzu haka, ana cigaba da tattara sakamakon zabe a matattarar zabe na karamar hukumar Kaduna ta kudu.

Zaben kananan hukumomi: PDP ta lallasa APC a akwatin mazabar Gwamna El-Rufa'i
Zaben kananan hukumomin Kaduna: PDP ta lallasa APC a akwatin mazabar Gwamna El-Rufa'i Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

An Ɗage Zaɓukan Ƙananan Hukumomi 4 a Jihar Kaduna

Mun kawo muku cewa hukumar zabe mai zaman kanta na Jihar Kaduna, KADSIECOM, ta dage zabukan kananan hukumomi da aka shirya yi a ranar Asabar a kananan hukumomi hudu a jihar saboda rashin tsaro.

Hukumar, a ranar Juma'a, ta ce an dage zabukan ne biyo bayan samun rahoton tsaro wadda ya nuna ba zai yi wu a gudanar da zabukan ba cikin lumana a kananan hukumomin Kajuru, Birnin Gwari, Chikun da Zangon Kataf.

Rahoton na Daily Trust ya ce Shugaban hukumar, Dr Saratu Binta Dikko-Audu ya ce dagewar ya zama dole ne domin kare rayyuka da dukiyoyin mutane harda ma'aikatan zaben da kayan aiki.

Asali: Legit.ng

Online view pixel