Matasan NYSC 5 sun rasa rayukansu sakamakon mumunan hadari a Abuja

Matasan NYSC 5 sun rasa rayukansu sakamakon mumunan hadari a Abuja

Mumunan hadarin mota yayi sanadiyar mutuwar matasa masu shirin bautan kasa biyar a titin Abaji-Kwali dake Abuja yayinda suka nufi zuwa sansanin NYSC.

Diraktar yada labarai na NYSC, Adenike Adeyemi, ta bayyana hakan a jawabin da ta saki ranar Laraba, rahoton Punch.

Tace:

"Cikin jimami da bakin ciki Dirakta Janar, da daukacin hukumar NYSC ke jajantawa iyalan matasan dake shirin fara bautan kasa da suka rasa rayukansu a hadarin motan da ya auku misalan karfe 2 na daren yau, Laraba, 28 ga Yuli, 2020, a babban titin Abaji/Kwali."
"Hakazalika Dirakta Janar da daukacin hukumar na jajantawa gwamnatin Akwa Ibom da Imo kan wannan hadari."

Karin bayani na nan tafe....

Matasan NYSC 5 sun rasa rayukan sakamakon mumunan hadari a Abuja
Matasan NYSC 5 sun rasa rayukan sakamakon mumunan hadari a Abuja
Asali: Original

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng