Gwamnatin Akwa Ibom ta sanya jarabawa ranar Sallah, Musulmai sun yi ca

Gwamnatin Akwa Ibom ta sanya jarabawa ranar Sallah, Musulmai sun yi ca

  • MURIC ta yi Alla-wadai da gwamnatin jihar Akwa Ibom
  • Ma'aikatar Ilmin jihar ta ce lallai ba zata dakatar da rubuta jarabawar shiga SS3 ba

Kungiyar kare hakkin Musulmai a Najeriya, MURIC, ta caccaki gwamnatin jihar Akwa Ibom kan hakikancewa kan rubuta jarabawar shiga sabon aji ranar Sallah.

Kungiyar MURIC tace gwamnatin Akwa Ibom bata shirya zama lafiya da mutanen sauran addinai a jihar ba.

Ma'aikatar Ilmin jihar Akwa Ibom ta sanar da cewa daliban dake jihar zasu cigaba da rubuta jarabawa.

Gwamnatin jihar tace jarabawar shiga SS3 a makarantun Sakandare za ta cigaba yau Sallah duk da cewa gwamnatin tarayya ta bada hutu.

MURC ta yi Alla-wadai da wannan abu da gwamnatin jihar keyi.

A jawabin da diraktan kungiyar MURIC, Farfesa Ishaq Akintola ya sake a shafin kungiyar, yace abinda gwamnatin tayi ya cika abin kunya.

Gwamnatin Akwa Ibom
Gwamnatin Akwa Ibom ta sanya jarabawa ranar Sallah, Musulmai sun yi ca Hoto

Yace:
"Mun girgiza kan irin nuna banbancin addinin da wasu gwamnatocin jiha ke yiwa Musulmai."

Kara karanta wannan

Kano: An sauke shugaban makaranta saboda ya bai wa dalibai hutun Sallah

"Gwamnatin jihar Akwa Ibom na sane sarai cewa akwai Musulmai yan asalin jihar da kuma baki. Akwai yaran Musulmai a makarantun Akwa Ibom."
"Hakikancewa kan cigaba da rubuta jarabawa a ranar ya nuna cewa gwamnatin jihar bata shirya zama lafiya da sauran addinai ba.
"Hakazalika MURIC na Alla-wadai da rainin hankalin gwamnatin Akwa Ibom na watsi da umurnin gwamnatin tarayya da ta bada hutu."

MURIC ta kara da cewa shin me za'a fadi da a Arewa akayi irin haka ranar Kirismeti.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng