Innalillahi: Tsohon malami a KADPOLY ya harba matarsa tare da kashe kansa

Innalillahi: Tsohon malami a KADPOLY ya harba matarsa tare da kashe kansa

- Ana zargin wani tsohon malamin KADPOLY da kashe kansa

- Sai da Austin Umera ya harbi matarsa, sannan ya kashe kansa

- Har yanzu ba a gano dalilin da zai sa babban mutum irinsa ya kashe kansa ba

Wani tsohon malamin KADPOLY, mai suna Austin Umera ya shayar da mutane mamaki a kan abinda ya aikata.

Ana zarginsa da laifin harbin matarsa, Dokta Maurin, wacce ita ma malama ce a jami'ar jihar Kaduna (KASU), inda daga bisani ya harbe kansa kuam ya fadi ya mutu.

Al'amarin ya faru ne a gidansu da ke layin Kigo a cikin garin Kaduna.

Yanzu haka Dokta Maurin tana kwance a asibitin sojoji na 44 da ke cikin Kaduna, inda ake cigaba da kulawa da lafiyarta.

An adana gawar mijinta a ma'adanar gawa dake asibitin kwararru na Barau Dikko a Tudun wada.

Jaridar Daily Trust ta samu labarin wannan mummuna al'amarin ne da misalin karfe 10 na daren Laraba.

Har ila yau, babu cikakke kuma gamsasshen bayani a kan silar aukuwa lamarin amma kakakin rundunar 'yan sandan jihar Kaduna, Mohammed Jalige ya tabbatar da aukuwar lamarin.

KU KARANTA: Matashi ya yi wa budurwa mugun duka tare da yunkurin kasheta a kan kudin da ya kashe mata a fitarsu ta farko

Innalillahi: Tsohon malami a KADPOLY ya harba matarsa tare da kashe kansa
Innalillahi: Tsohon malami a KADPOLY ya harba matarsa tare da kashe kansa. Hoto daga @daily_trust
Asali: UGC

KU KARANTA: Hotunan budurwar da tsohon kwamishinan dan sanda ya fizge wa kunne da cizo

A wani labari na daban, kowa yana da ra'ayi da zabi idan aka zo batun soyayya, amma yawancin mutane su kan duba aljihu.

Wata budurwa, mai suna Rutie, ta janyo cece-kuce a kafar sada zumuntar zamani ta Twitter, bayan ta bai wa matasa shawara a kan soyayya.

Kamar yadda Rutie ta ce, duk saurayin da bashi da a kalla naira miliyan 25 a asusunsa, bai dace da soyayya ba.

Nan da nan samari da 'yan mata suka yi ta tururuwa suna yin tsokaci a karkashin wallafar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng