Gwamnati ta hana zamanta da Kungiyar ASUU ya tafi salin-alin inji Ogunyemi
- ASUU ta ce Gwamnatin Tarayya ba ta da niyyar kawo karshen yajin-aikinta
- Malaman Jami’ar sun zargi Gwamnati da hana tattaunawar tafiya da kyau
- Shugaban ASUU ya ce kin amince wa da manhajar UTAS ya tsaida magana
Shugaban kungiyar ASUU na kasa, Farfesa Biodun Ogunyemi, ya bayyana haka a lokacin da aka yi hira da shi a shirin Politics Today a gidan talabijin na Channels.
Farfesa Biodun Ogunyemi ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta ki daukar matakan da su ka dace na ganin an janye dogon yajin aikin da ake yi a jami’o’i.
KU KARANTA: Bukatu 6 da ASUU ta kai gaban teburin Shugaba Buhari
Biodun Ogunyemi ya ce jinkirin da gwamnati ta ke yi wajen amince wa da manhajar UTAS da malamai su ka kirkiro, shi ne babban abin da ya ke jawo cikas.
Ya ce: “Har yanzu ana yajin-aiki a dalilin kin gwamnati na daukar matakan da su ka dace. Mun ba su makonni biyu su duba bukatu biyar da mu ka gabatar.”
“Mun zauna da gwamnati, amma ba ta da niyyar kawo karshen lamarin. Sun samu tsawon shekara su duba lamarin. Amma sun yi mana tayin abin da ba mu dauka ba.”
Farfesan ya ce sun gabatar da UTAS gaban Ministan ilmi, shugabannin majalisar dattawa da ofishin babban akawun gwamnati, kuma sun yi na’am da manhajar.
KU KARANTA: Ko UTAS, ko rijiya, ASUU ta ce Allan-barin ba za ta shiga IPPIS ba

Asali: UGC
“Mun kusa samu a amince da UTAS, sai kuma gwamnati ta ke cewa mu fara shiga IPPIS, daga nan sai a koma UTAS. Babu hankali a wannan!” inji Farfesan.
“Sun ce za a biyamu idan mun koma IPPIS.” ASUU ta ce malaman jami’a ba za su yarda da hakan ba.
A watan jiya Ministan kwadago, Dr. Chris Ngige ya bayyana cewa Ministocin kudi, ilimi, kwadago da ofishin babban akawun gwwamnati za su zauna da ASUU.
Ma’aikatan Jami’an su na kuka a kan tsarin IPPIS, sun kuma ce an hana su wasu alawus da kudin gyara jami'o'i. Har yanzu ba a iya shawo kan bakin zaren ba.
Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Asali: Legit.ng