Zanga-zanga: Ganduje ya gabatar da wata muhimmiyar bukata a gaban Rarara da Ali Nuhu

Zanga-zanga: Ganduje ya gabatar da wata muhimmiyar bukata a gaban Rarara da Ali Nuhu

- Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano, ya tunkari masana'antar shirya fina-finai domin su taimaka masa wajen tabbatar da zaman lafiya a jiharsa

- Ganduje ya nemi Rarara da Ali Nuhu su yi amfani da kwarewarsu wajen shirya fim da yin wakar wayar da kai ga al'umma don jadadda masu muhimmancin zaman lafiya

- Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun tashe-tashen hankula a wasu sassan kasar sakamakon zanga-zangar EndSARS

Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, a kokarin da yake na ganin an samu zaman lafiya a jihar, ya roki kungiyar masu shirya fina-finan Hausa da na mawaka a kan su yi amfani da kwarewarsu wajen wayar da kan al’umma game da muhimmancin zaman lafiya.

Ya yi wannan kira ne a yayin wata ganawa da ya yi da kungiyar MOPAN a ranar Talata, a dakin taro na Africa House da ke gidan gwamnatin jihar, jaridar Aminiya ta ruwaito.

Zanga-zanga: Ganduje ya gabatar da wata muhimmiyar bukata a gaban Rarara da Ali Nuhu
Zanga-zanga: Ganduje ya gabatar da wata muhimmiyar bukata a gaban Rarara da Ali Nuhu Hoto: real_rarara_multimedia
Asali: Instagram

A cikin jawabin nasa, gwamnan ya yi kira ga shahararren mawakin nan na siyasa, Dauda Kahutu wanda aka fi sani da Rarara, a kan ya rera wakokin wayar da kai ga jama’a kan muhimmancin zaman lafiya.

KU KARANTA KUMA: Boko Haram: An kashe mutum 20 yayinda aka jikkata 10 a jihar Borno

Har ila yau, ya bukaci fitaccen jarumi a masana’antar Kannywood, Ali Nuhu, da ya shirya fina-finan wayar da kan al’umma kan fa’idar zaman lafiya.

Ana dai ta fuskantar rashin zaman lafiya a wasu jihohin kasar sakamakon zanga-zangar EndSARS da aka fara gudanar da ita makonni biyu da suka gabata.

KU KARANTA KUMA: Ana tsaka da rabon tallafin korona, 'yan daba suka buga wawaso

A gefe guda, mun ji cewa, an yi kira ga sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero a kan ya sanya baki domin kawo karshen zanga-zangar da matasa ke yi a jihar.

Ministan tsaro, Bashir Magashi da takwaransa na noma, Sabo Nanono, wadanda suka kasance yan asalin jihar ne suka yi wannan kira.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng