Da ɗuminsa: Yan ta'adda sun kaiwa jami'an ƴan sandan RRS hari a Lagos

Da ɗuminsa: Yan ta'adda sun kaiwa jami'an ƴan sandan RRS hari a Lagos

- Wasu batagari da ake zargin yan daba ne sun kaiwa jami'an yan sandan RRS hari a jihar Lagas

- Lamarin ya afku ne a yau Litinin, 19 ga watan Oktoba

- Yan iskan sun yi zargin cewa an turo jami'an ne domin su dakatar da zanga-zangar kawo karshen SARS da ake gudanarwa

Wasu yan daba a ranar Litinin, sun kai hari kan jami’an rundunar yan sandan RRS a jihar Lagas.

Harin ya gudana ne a hanyar Herbert Macaulay, da ke yankin Yaba a jihar.

Ana ta samun barkewar rikici a wasu yankunan kasar yayinda ake tsaka da zanga-zangar #ENDSARS.

A cewar wani idon shaida, yan iskan sun farma jami’an tsaron kan hasashen cewa an turo su ne domin su dakatar da zanga-zangar.

Da ɗuminsa: Yan ta'adda sun kaiwa jami'an ƴan sandan RRS hari a Lagos
Da ɗuminsa: Yan ta'adda sun kaiwa jami'an ƴan sandan RRS hari a Lagos Hoto: @TheNationNews
Asali: Twitter

An gano yan daban suna wurgin motocin tawagar ta RRS da duwatsu da sanduna yayinda jami’an suka tarwatse domin neman mafaka.

KU KARANTA KUMA: Sauya salon zanga-zanga: An sako sojoji zuwa titunan Abuja

Mutuwa Adejobi, jami’in hulda da jama’a na rundunar a jihar, bai amsa kiran da aka masa ba don jin ta bakinsa game da lamarin.

A ranar Alhamis da ta gabata, yan iska sun farma masu zanga-zangar a kofar majalisar dokokin jihar da ke Ikeja.

Lamarin ya yi sanadiyar raunata masu zanga-zanga da dama.

A wani labarin kuma, Gwamnatin jihar Edo ta sanar da sanya dokar hana fita na sa’o’i 24 a fadin jihar.

KU KARANTA KUMA: COVID-19: Sabbin mutane 133 sun kamu da Korona, mutane 2 sun mutu nan take

Dokar za ta fara aiki daga karfe 4:00pm na ranar 19 ga watan Oktoba, har sai baba-ta-gani. Babban sakataren gwamnatin jihar, Osarodion Ogie ne ya fitar da sanarwar, Channels TV ta ruwaito.

Ogie ya bayyana cewa an sanya takunkumin ne sakamakon hare-haren da wasu yan iska da suka mamaye zanga-zangar #ENDSARS suka aiwatar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng