Watakila Cristiano Ronaldo ya keta ka’idar COVID-19 – Ministan wasannin Italiya

Watakila Cristiano Ronaldo ya keta ka’idar COVID-19 – Ministan wasannin Italiya

- Gwamnatin Italiya ta yi magana game da lamarin Cristiano Ronaldo

- ‘Dan wasan gaban Juventus mai shekaru 35 ya kamu da Coronavirus

- Ministan kasar ya na zargin ‘dan wasan bai bi ka’idar takaita cutar ba

AFP ta ce akwai yiwuwar Cristiano Ronaldo ya saba dokar yaki da annobar COVID-19 da dawowansa Italiya da ya yi bayan ya kamu.

Ministan wasanni na Italiya, Mista Vincenzo Spadafora, ya yi magana a ranar Alhamis game da dawowar Ronaldo daga kasar Portugal.

Game da saba doka, da aka tambayi Ministan, sai ya ce: “Eh, ina tunanin haka, idan babu tabbatacciyar izini daga hukumomin lafiya.”

KU KARANTA: Ronaldo ya na cikin 'yan wasan da su ka fi kudi a Duniya

‘Dan wasan mai shekaru 35 ya kinkimo jirgin sama ya shigo Arewacin Italiya bayan an tabbattar da cewa ya na dauke da kwayar COVID-19.

Ana zargin ‘dan wasan da saba doka ganin yadda wasu ma’aikatan kungiyar kwallon kasan Juventus su ka kamu da Coronavirus a makon nan.

Amma kungiyar Juventus ta ce: “Cristiano Ronaldo ya dawo Italiya ne a jirgi bayan hukumomin lafiya sun tabbatar ‘dan wasan zai killace kansa.”

KU KARANTA: 'Dan wasa Ronaldo ya saye gidan da kowa zai yi kauyanci a ciki

Watakila Cristiano Ronaldo ya keta sharudan COVID-19 inji Ministan wasannin Italiya
Tauraro Cristiano Ronaldo Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

Ministan wasanni, Spadafora ya ce har yanzu dokar gwamnati ta na aiki, kuma har ga ‘yan kwallo.

Yanzu haka duka ‘yan wasan Juventus su na killace, a dalilin kamuwa da cutar da Ronaldo da kuma ‘dan wasa Weston McKennie su ka yi.

A farkon makon nan ne aka yi gwaji inda aka tabbatar da cewa Cristiano Ronaldo ya kamu da cutar Coronavirus lokacin da ya ke wasa a gida.

Hukumar kwallon kafa na kasar Portugal ta sanar da haka a wani fitar da jawabi da ta fitar.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel