Gwamnatin Nigeria za ta haramta shigo da madara daga 2022 - Ministan noma

Gwamnatin Nigeria za ta haramta shigo da madara daga 2022 - Ministan noma

- Sabo Nanono,ministan noma ya jadadda aniyar gwamnatin tarayya na haramta shigo da madara cikin kasar

- Nanono ya ce daga shekarar 2022 ko shakka babu za a daina shigo da madara domin ma’aikatarsa na shirye-shiryen samar da hanyoyin sarrafa ta a cikin gida

- Zuwa yanzu ya kuma ce Najeriya ce kan gaba a wajen samar da shinkafa da rogo a duniya

Ministan noma da raya karkara, Sabo Nanono, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya za ta haramta shigo da madara cikin kasar daga shekarar 2022.

Nanono ya bayyana hakan ne a yayinda yake zantawa da manema labarai a Abuja, a wani taro kan ranar abinci ta duniya na 2020.

Ya yi bayanin cewa ma’aikatar na shirye-shirye domin tabbatar da samar da kayayyaki don samar da madara, jaridar The Cable ta ruwaito.

Gwamnatin Nigeria za ta haramta shigo da madara daga 2022 - Ministan noma
Gwamnatin Nigeria za ta haramta shigo da madara daga 2022 - Ministan noma Hoto: @thecableng
Asali: Twitter

“Muna shirye-shirye a wannan ma’aikata kuma ku zuba ido ku ga abunda na fadi, a shekaru biyu masu zuwa za mu haramta shigo da madara cikin kasar nan. Kuma ku tambaye ni dalili: Muna da shanaye miliyan 25 a kasar nan da za su samar da madara lita miliyan biyar a kullun,” in ji shi.

KU KARATA KUMA: Da ɗuminsa: APC ta kori ƴar majalisar ta mace tilo saboda zargin cin amana

“Matsalar a yanzu shine kayayyakin amfani, wanda mun fara shirye-shiryen dasa hanyar sarrafa madara a fadin kasar. Ban ga dalilin da zai sa mu shigo da madara a shekaru biyu masu zuwa ba. Ya kamata mu daina shigo da madara.”

Nanono ya kuma ce a yanzu Najeriya ce ke samar da shinkafa da rogo mafi girma a duniya.

Ya ce: “Najeriya ta habbaka shirin samar da shinkafa domin karfafa harkar noman shinkafa a cikin gida sannan ta tsare hanyar shigo da yar waje.”

KU KARANTA KUMA: Ta’addanci: Yan gudun hijira na iya komawa Baga domin akwai tsaro yanzu, gwamnatin Borno

Ministan ya ci gaba da bayyana cewa farashin kayayyaki da ya hau a yanzu saboda annobar COVID-19 zai sauko a yan watanni masu zuwa.

A gefe guda, gwamnatin tarayya zata kirkiri ayyuka miliyan 10 a fannin noma da kiwo ta shirin noma don abinci da samun ayyuka (AFJP).

Ministan noma, Muhammad Nanono ya fadi hakan a ranar Talata a Abuja lokacin da ake wata tattaunawa da shi akan shirye-shiryen murnar ranar Abinci ta duniya dake gabatowa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng