Bai kamata a saurari ma su zanga-zangar ENDSARS ba - Bidiyon Jarumi Zaharaddeen Sani

Bai kamata a saurari ma su zanga-zangar ENDSARS ba - Bidiyon Jarumi Zaharaddeen Sani

- Jarumi a masana'antar shirya fina-finan Hausa (Kannywood), Zaharaddeen Sani, ya bayyana ra'ayinsa a kan zanga-zangar ENDSARS

- Zangar-zangar neman a soke rundunr SARS ba ta samu karbuwa ba a jihohin arewa maso yamma da arewa maso gabas

- Wasu matasa a Maiduguri, babban birnin jihar Borno, sun gudanar da zanga-zangar nuna goyon bayan rundunar SARS

Zaharadden Sani, Jarumi a masana'antar shirya fina-finan Hausa (Kannywood), ya ce a tunaninsa kuskure ne jama'a su ke gudanar da zanga-zanga a kan jami'an 'yan sanda ba 'yan bindiga da ke kashe mutane ba

A cikin wani faifan bidiyo da Legit.ng Hausa ta ci karo da shi a dandalin sada zumunta, an jiyo Jarumin ya na bayyana cewa; "sai jami'an 'yan sanda za a yi wa zanga-zanga, me ya sa jama'a ba za su yi wa gwamnati zanga-zanga ba saboda 'yan ta'adda sai saboda dan SARS guda daya,?

"Ko su 'yan bindiga tsoronsu ake ji? su na kashe mutane ba iyaka, amma ba za a iya fitowa a yi zanga-zanga saboda hakan ba, sai saboda laifin dan SARS guda daya.

DUBA WANNAN: Yan sanda sun kashe masu zanga zangar EndSARS guda 10 - Amnesty

"Ni a ganina hakan kuskure ne, bai kamata shugaban rundunar 'yan sanda ya sauraresu ba, ya fada mu su cewa aiki ya yi ma sa yawa, akwai aiyuka a gabansa da yawa, saboda 'yan bindiga su na ta kashe mutane," kamar yadda Jarumin ya bayyana.

Bai kamata a saurari ma su zanga-zangar ENDSARS ba - Bidiyon Jarumi Zaharaddeen Sani
Wasu ma su zanga-zangar ENDSARS
Asali: UGC

A ranar Litinin ne Legit.ng Hausa ta wallafa cewa a wani faifan bidiyo da jaridar The Cable ta wallafa an ga wasu ma su zanga-zanga sun hada kai tare da ceton wani dan sanda da wasu 'yan daba ke nufin cutarwa.

DUBA WANNAN: Kaduna: 'Yan bindiga sun kashe basarake Alhaji Musa Abubakar a gidansa

Duk da babban sifeton rundunar 'yan sanda (IGP) ya sanar da cewa an rushe rundunar SARS, har yanzu fusatattun matasa ba su daina fitowa domin gudanar da zanga-zanga ba.

A yayin da matasan ke cigaba da gudanar da zanga-zangar, wasu matasa a Maiduguri, babban birnin jihar Borno, sun gudanar da zanga-zangar nuna goyon bayan rundunar SARS a ranar Talata.

Matasan sun bukaci a dawo da SARS sannan a tura jami'an rundunar zuwa jihar Borno domin su yaki 'yan Boko Haram.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng