Daga ƙarshe: Kotu ta ci tarar Sanata Abbo N50m saboda cin zarafin wata mace

Daga ƙarshe: Kotu ta ci tarar Sanata Abbo N50m saboda cin zarafin wata mace

- Kotun birnin tarayya ta ci tarar Sanata Elisha Abbo naira miliyan 50 kan cin zarafin wata mata

- An dai kama Abbo da laifin marin matar a wani shagon siyar da kayan jima’i a Abuja

- Abbo dai shine sanata mai wakiltan Adamawa ta arewa a majalisar dattawa

Wata babbar kotun tarayya ta umurci Elisha Abbo, Sanata mai wakiltan Adamawa ta arewa, da ya biya miliyan N50 a matsayin diyya ga Osimibibra Warmate kan cin zarafinta.

A 2019, hukumar yan sanda ta gurfanar da Abbo a gaban wata kotun majistare da ke Zuba, kan wata tuhuma guda da ake masa na cin zarafin Warmate a shagon siyar da kayan jima’i a Abuja.

Duk da hujja na bidiyon lamarin da aka gabatar, Abdullahi Ilelah, alkalin kotun, ya riki takardar babu kara da dan majalisar ya gabatar, sannan ya kori shari’ar.

Daga ƙarshe: Kotu ta ci tarar Sanata Abbo N50m saboda cin zarafin wata mace
Daga ƙarshe: Kotu ta ci tarar Sanata Abbo N50m saboda cin zarafin wata mace Hoto: @thecableng
Source: Twitter

Sai dai kuma, Warmate ta shigar da karar neman yanci a gaban babbar kotun tarayya.

Da yake zartar da hukunci a ranar Litinin, alkalin ya kama Abbo da laifi sannan ya umurce shi da ya biya mai karar miliyan N50, jaridar The Cable ta ruwaito.

Lugard Tare-Otu da Nelson wadanda suka bayyana kansu a matsayin lauyoyin Warmate sun tabbatar da hukuncin kotun a shafin Twitter.

Kun tuna wannan bidiyon sanatan Najeriya da ya mari wata matashiyar mata a shago? Toh gaskiya ta yi halinta a yau inda kotu ta ci tarar sanatan N50M. Ina farin cikin wakiltan wannan matashiya a wannan kara,” in ji Nelson.

A wani labarin, ranar Litinin, kwararru a Majalisar Dinkin Duniya sun bukaci Nigeria da ta saki mawakin da aka yankewa hukuncin kisa saboda zarginsa da batanci ga Annabi Muhammad (SAW).

A watan da ya gabata ne wata kotun shari'a a Kano, ta yankewa Yahaya Aminu Sharif hukuncin kisa, bayan da ya yi wakar batanci ga Musulunci da Annabi.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng