Yaran mu na shiga Boko Haram saboda rashin aikin yi - Gwamna Zulum

Yaran mu na shiga Boko Haram saboda rashin aikin yi - Gwamna Zulum

- Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya janyo hankalin 'yan majalisa game da halin da 'yan gudun hijira ke ciki a Borno

- Zulum ya bayyana cewa yara a jihar Borno suna shiga kungiyar ta'addanci na Boko Haram saboda babu ayyukan yi duba da cewa an raba su da gonakinsu

- Gwamnan ya yi gargadin cewa idan ba a dauki matakin taimaka musu na dindindin su koma gidajensu lafiya ba matsalar da ke tafe sai ta fi na yanzu

Yaran mu na shiga Boko Haram saboda rashin aikin yi - Gwamna Zulum
Yaran mu na shiga Boko Haram saboda rashin aikin yi - Gwamna Zulum. Hoto daga AFP
Source: Twitter

DUBA WANNAN: An kama ɗan sanda bayan budurwarsa ta mutu a otel ɗin da suka kwana tare

Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Zulum ya yi gargadin cewa ana shigar da yara a Borno cikin kungiyar ta'addanci na Boko Haram.

Gwamnan ya yi wannan furucin ne yayin da ya ke tarbar wata kwamiti na mambobin 'yan majalisar wakilai a ofishinsa da ke Maiduguri a babban birnin jihar Borno.

Zulum ya ce shigar yaran cikin kungiyar ta Boko Haram na da alaka da rashin ayyukan yi a jihar, inda ya kuma ce akwai fiye da mutane 700,000 a sansanin 'yan gudun hijira a Monguna sannan akwai wasu 400,000 da aka raba su da gonakinsu.

KU KARANTA: Hotuna: Wani mutum ya auri surukarsa bayan rabuwa da matarsa

Ya ce;

"Hanyar daya da za a magance matsalar shine mu tabbatar mutanen mu sun koma gidajensu cikin mutunci. Idan ba a dauki mataki a kai ba ina tabbatar muku za mu fuskanci kallubalen da ya fi abinda muke fama da shi yanzu.

"Domin a yanzu 'yan ta'adda na shigar da yaran mu cikin kungiyarsu saboda karuwar rashin ayyukan yi."

Gwamnatin Jihar Borno ta bada shawarar cewa hanyar da za a magance wannan matsalar shine a mayar da hankali wurin daukan matakan taimaka wa mutanen na dindindin su samu su koma gidajensu lafiya a maimakon basu tallafi idan abu ya faru sai kuma a manta da su.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164

Tags: