Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)

Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)

A ranar Alhamis, shugaban kasar Burkina Faso, Roch Kabore, ya kawo wa shugaban kasa Muhammadu Buhari ziyara ta musamman, a fadar shugaban kasa, Abuja.

Sanarwar hakan ta fito daga bakin hadimin shugaban kasar ta fuskar gidajen Radio, Talabijin da kafofin sadarwa, Buhari Sallau, da ya wallafa a shafinsa na Twitter.

KARANTA WANNAN: Nigeria ta samu babban ci gaba a kwallon duniya, ita ce ta 29 - FIFA

Buhari Sallau ya wallafa cewa "Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karbi bakuncin shugaba Roch Kabore na kasar Burkina Faso, a fadar shugaban kasa, ranar 17 ga watan Satumba, 2020."

Duba hotunan ziyarar a kasa:

Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)
Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)
Asali: Twitter

Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)
Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)
Asali: Twitter

Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)
Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)
Asali: Twitter

Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)
Yanzu yanzu: Shugaban kasa Buhari ya marabci shugaban kasar Burkina Faso (Hotuna)
Asali: Twitter

A wani labarin, Kungiyar kwallon kafar Nigeria, Super Eagles ta haura zuwa mataki na 29 a jadawalin kungiyoyin kwallon kafa na kasashen duniya, amma har yanzu itace ta uku a kasashen Africa.

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin sabon jadawalin da hukumar kula da kwallon kafa ta duniya FIFA ta wallafa a ranar Alhamis.

Babu wani canji da aka samu a jadawalin kasashen Africa, inda Senegal ta ke kan gaba, yayin da Carthage Eagles ta Tunisia ke na biyu, sai Nigeria na Uku.

KARANTA WANNAN: Ƴan bindiga sun kai wa ƴan sanda hari a Sokoto 'sun kashe DPO'

Kasar Algeria ce ta uku, sai kuma kasar Morocco a na biyar, jadawalin kungiyoyin kwallon kafa na Afrika da ya jima bai canja ba.

Haka zalika, a bagaren jadawalin na matakin duniya baki daya, kasar Belgium, France, Brazil da England sune a rukunin 1 zuwa 4, yayin da Potrugal ta zakuda zuwa na 5 da ga ta 7.

Sai dai abokan karawar Super Eagles a tankaden gasar AFCON 2021, ba su samu ci gaba ba. Ya yin da Benin Republic da Leostho suka ci gaba da zama na 84 da 139, sai Sierra Leone da ta sauko zuwa ta 119.

A daya hannun, babu wani ci gaba da Cape Verde, Central Africa Republic da Leberia suka samu. Cape Verde na a lamba ta 78, CAR ita ce ta 110, yayin da Leberia ta koma ta 152.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel