Cigaba: Ganduje ya saka na'urorin sa-ido a manyan titunan Kano, bidiyon yadda suke aiki

Cigaba: Ganduje ya saka na'urorin sa-ido a manyan titunan Kano, bidiyon yadda suke aiki

Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya kammala saka na'urorin sa-ido a kan wasu daga cikin manyan titunan birnin Kano domin inganta tsaro da saukakawa jami'an tsaro aiki.

A wani takaitaccen sako da Salihu Tanko Yakasai, hadimin Ganduje, ya wallafa a shafinsa na tuwita, an nuna bidiyon yadda jami'an 'yan sanda ke kallon motsin mutane da ababen hawa a manyan titunan.

"Duk da Kano tana cikin jihohin da ke da zaman lafiya a Najeriya a shekaru 5 da suka gabata, mai girma gwamna Abdullahi Umar Ganduje bai daina kokarin kara karfafa tsaro a jihar Kano ba, saboda gwamnatinsa ta saka na'urorin sa-ido a manyan titunan birnin Kano.

"Ana sarrafa na'urorin daga dakin na musamman a hedikwatar 'yan sandan Kano," kamar yadda Yakasai ya bayyana.

Ko a kwanakin baya gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da cewa ta saka irin wadannan na'urori a cikin birnin Kaduna domin inganta tsaro.

Jama'a da dama da suka yi magana a kan sakon da Yakasai ya wallafa, sun yabawa kokarin gwamna Ganduje na zamanantar da tsaro a Kano.

Cigaba: Ganduje ya saka na'urorin sa-ido a manyan titunan Kano, bidiyon yadda suke aiki
Ganduje
Source: UGC

Wasu daga cikinsu sun yi kira da sauran gwamnonin jihohin arewa su yi koyi da irin wannan cigaba da Ganduje ya kawowa Kano, a cewarsu, hakan zai taimaka wajen saurin gano batagari da kuma daukan mataki a kan lokaci.

KARANTA: Buhari zai kaddamar da shirin tallafawa 'yan kasuwa da N50,000 a kowanne wata

KARANTA: Bikin Hanan: 'Ba kai mana adalci ba' - Aisha Buhari ta koka a kan wanda ya yi zanen barkwanci

A daren ranar Lahadi ne hedikwatar rundunar tsaro ta kasa (DHQ) ta sanar da cewa ta tsaurara matakan tsaro a Abuja da wasu makwabtan jihohi bayan samun labarin cewa kungiyar Boko Haram tana shirin kai wasu hare-hare.

DHQ ta ce ta gaggauta daukan wannan mataki ne bayan hukumar kwastam ta Najeriya (NCS) ta fitar da wata sanarwa domin ankarar da mazauna Abuja da wasu makwabtan jihohi a kan shirin kai hare-haren.

Manjo Janar John Enenche, kakakin DHQ, ya ce rundunar soji ta sanar da dukkan dakarunta su kasance cikin shirin 'ko ta kwana'.

A cikin wata sanarwa da hukumar Kwastam ta fitar, ta ce mayakan kungiyar Boko Haram suna shirin kaddamar da wasu hare-hare a Abuja, jihar Kogi da kuma jihar Nasarawa.

Sai dai, a cikin jawabin da Enenche ya fitar ranar Lahadi, DHQ ta bayyana cewa za ta yi kokarin dakile kai hare-haren.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng