Soji sun gano masana'antar hada bama-bamai a Nasarawa, an damke mutum 410

Soji sun gano masana'antar hada bama-bamai a Nasarawa, an damke mutum 410

Hukumar Sojin Najeriya a ranar Laraba ta ce daruruwan mambobin sabuwar kungiyar yan ta'adda, Darul Salam da ta fara tsirowa a jihar Nasarawa sun mika wuya.

Hakazalika jami'an Soji sun gano masana'antar kera bama-bamansu kuma sun ragargaza.

Hakan na kunshe cikin jawabin da kakakin hukumar Soji, Manjo Janar John Enenche, ya saki.

Eneche yace sun mika wuya ne bayan hare-haren da dakarun atisayen Operation Whirl Stroke suka kai tare da hadin kan jami'an wasu hukumomin tsari a garin Uttu, karamar hukumar Toto a jihar Nasarawa.

Daga cikin yan ta'addan akwai mata da yara.

Kakakin Sojin ya ce a ranar 25 ga Agusta, 2020, akalla yan ta'addan 410, suka mika wuya.

Bayan haka, jami'an Sojin Operation Whirl Stroke sun dira masana'antar kera bama-bamansu kuma aka gano makamai da rokoki da dama.

Soji sun gano masana'antar hada bama-bamai a Nasarawa, an damke mutum 410
Soji sun gano masana'antar hada bama-bamai a Nasarawa, an damke mutum 410
Asali: Facebook

A cewar jawabin: "Bayan hakan, Dakarun Operation WHIRL STROKE yayinda suke sintiri a Uttu, a ranar 26 ga Agusta 2020 sun dira masana'antar kera bama-baman kungiyar yan ta'addan Darul Salam."

"Yayin farmakin, Sojoji sun gano kayayyakin hada bama-bamai a wajen wanda ya hada da na'urar harba roka 6, buhun taki daya, buhun garin bindiga daya, gurnet 10, RPG daya, bama-mamai 2, rokoki 13 dss.

"Sai muka yi raga-raga da masana'antar yayinda Sojoji suka cigaba da binciken cikin daji domin kama sauran yan ta'addan dake kokarin guduwa." Enenche yace.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng