Faɗa ta kaure tsakanin magoya bayan APC da ADC a Ondo, an raunata mutane da dama

Faɗa ta kaure tsakanin magoya bayan APC da ADC a Ondo, an raunata mutane da dama

Ƙazamin rikici ya ɓarke tsakanin tsakanin magoya bayan jam'iyyar All Progressives Congress, APC da na African Democratic Congress, ADC, a garin Yaba da ke jihar Ondo.

The Punch ta ruwaito cewa mutane da dama sun samu raunuka kuma an lalata a ƙalla ababen hawa 15 a fadar da ta fara a yammacin ranar Alhamis.

Rikicin ya barke ne sa'o'i kadan kafin a fara zabukkan kananan hukumomi a jihar.

Faɗa ta kaure tsakanin magoya bayan APC da ADC a Ondo, an raunata mutane da dama
Faɗa ta kaure tsakanin magoya bayan APC da ADC a Ondo, an raunata mutane da dama. Hoto daga The Punch
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Za a yi wa matar da ta kashe dan ta a Kano gwajin kwakwalwa

A halin yanzu dai ba a tabbatar da dalilin da ya janyo rikicin ba a lokacin haɗa wannan rahoton amma an gano cewa rikicin ba zai rasa nasaba da zaɓen kananan hukumomi da za ayi a ranar Asabar mai zuwa ba.

Ku saurari ƙarin bayani...

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164