Riham Yaqoob: Kyakkyawar budurwa da aka harbe a kasar Iraqi a yayin da take kokarin kare hakkin al'ummar kasar

Riham Yaqoob: Kyakkyawar budurwa da aka harbe a kasar Iraqi a yayin da take kokarin kare hakkin al'ummar kasar

Wasu 'yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun harbe wata kyakkyawar budurwa mai suna Riham Yaqoob a birnin Basra, biyo bayan zanga-zangar da take jagoranta dake kalubalantar gwamnatin kasar

Riham Yaqoob, wata kyakkyawar budurwa ce 'yar kasar Iraqi da take rajin kare hakkin dan adam, kuma likita ce da ta jagoranci zanga-zangar nuna rashin goyon baya ga gwamnatin kasar.

A ranar Laraba 19 ga watan Agustan nan ne dai aka harbe budurwar a garin Basra dake kasar ta Iraqi.

An harbe wata kyakkyawar budurwa mai rajin kare hakkin dan adam a kasar Iraqi
An harbe wata kyakkyawar budurwa mai rajin kare hakkin dan adam a kasar Iraqi
Asali: Facebook

Bayan harbe Riham, firaim ministan kasar Mustafa al-Kadhimi ya kori shugaban hukumar 'yan sandan birnin na Basra da kuma wasu daga cikin jami'an tsaro. Haka kuma yayi alkawarin yin iya bakin kokarinshi wajen tabbatar da cewa jami'an tsaro sunyi abinda ya kamata.

Firaministan ya ce:

"Abinda 'yan bindigar suka yi da kuma barazanar da suka zama baza mu yadda da ita ba, saboda haka zamu yi duk abinda ya kamata daga kan ma'aikatar cikin gida ma'aikatar tsaro waje domin ganin sun tashi tsaye wajen kare al'umma da dukiyoyinsu daga 'yan ta'addar."

An harbe wata kyakkyawar budurwa mai rajin kare hakkin dan adam a kasar Iraqi
An harbe wata kyakkyawar budurwa mai rajin kare hakkin dan adam a kasar Iraqi
Asali: Facebook

KU KARANTA: Na yiwa mijina dukan tsiya ne saboda yana raina mini wayo da yawa - Matar aure ta sanar da kotu

Wannan dai na zuwa ne watanni biyar kacal bayan Kadhimi, tsohon shugaban tsaron ya shiga ofis bayan murabus da magabacinshi yayi akan zanga-zangar da ake yi a garin Baghdad babban birnin kasar, birnin Basra da kuma wasu daga cikin biranen kudancin kasar.

Ana cigaba da zanga-zanga a Iraqi sakamakon cin hanci da yayi kaka gida a kasar, rashin aikin yi da dai sauran su.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel