Hotuna: Tsohon Sarkin Kano Sanusi II ya tafi Senegal don hallartar jana'izar ɗan Sheikh Inyass

Hotuna: Tsohon Sarkin Kano Sanusi II ya tafi Senegal don hallartar jana'izar ɗan Sheikh Inyass

- Tsohon Sarkin Kano, Sanusi II ya shilla birnin Kaolack da ke Senegal a yau Alhamis

- Muhammadu Sanusi II ya tafi kasar ne domin hallartar jana'izar Sheikh Tijjanni Nyass

- Marigayin ya rasu ne a ranar Litinin yana da shekaru 65 a duniya

Tubabben tsohon sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, a ranar Alhamis ya bar Najeriya Najeriya don zuwa Kaolack, Senegal inda zai hallarci jana'izar Sheikh Tijjani Nyass dan Sheikh Ibrahim Nyass.

Marigayin Malamin ya rasu ne a ranar Litinin yana da shekaru 65.

Hotuna: Tsohon Sarkin Kano Sanusi II ya tafi Senegal don hallartar jana'izar ɗan Sheikh Inyass
Tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II. Hoto daga Daily Nigerian.
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: COVID-19: Buhari ya sabunta dokar kulle da makonni hudu

Hotuna: Tsohon Sarkin Kano Sanusi II ya tafi Senegal don hallartar jana'izar ɗan Sheikh Inyass
Muhammadu Sanusi II. Hoto daga Daily Nigerian
Asali: Twitter

A sakon ta'aziyarsa ga Shugaba Macky Sall, gwamnati da al'ummar Senegal da dimbin mabiya darika Tijaniyya a Najeriya, Shugaba Buhari ya nuna bakin cikinsa game da rasuwar malamin.

Buhari ya ce, "Mun yi bakin samun labarin rasuwar Khalifa, Sheikh Ahmed Nyass da ya rasu a Senegal.

"Sheikh Ahmed Nyass da ya gaji mahaifinsa, Sheikh Ibrahim Nyass bai bawa mabiya mahaifinsa kunya ba.

"Za a rika tuna wa da shi saboda dimbin hidiman da ya yi wa addinin islama da mabiya darikarsa har da wadanda ke Najeriya."

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164