Karin 'yan Najeriya 457 sun kamu da korona, jimilla 44,890

Karin 'yan Najeriya 457 sun kamu da korona, jimilla 44,890

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 457 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:37 na daren ranar Laraba 5 ga Augustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 457 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Lagos-137

FCT-76

Plateau-40

Rivers-35

Enugu-34

Oyo-25

Abia-23

Delta-12

Edo-11

Ebonyi-11

Cross River-10

Kwara-10

DUBA WANNAN: Yaki da COVID-19: Ganduje ya zama gwarzo a tsakanin gwamonin Najeriya

Kaduna-9

Anambra-7

Ogun-5

Imo-3

Bauchi-3

Osun-2

Nasarawa-2

Kano-1

Ekiti-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Laraba 5 ga watan Agusta shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 44,890 .

An sallami mutum 32,165 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 927.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel