IPMAN ta umurci gidajen mai su fara sayar da mai a farashin N150

IPMAN ta umurci gidajen mai su fara sayar da mai a farashin N150

Kungiyar yan kasuwan man fetur masu zaman kansu IMAN, shiyar jihar Kano, ta umurci mambobinta su fara sayar da man fetur a farashin N150 ga lita.

Daily Nigerian ta ce a jawabin da ya saki, shugaban kungiyar na jihar Kano, Bashir Dan-Mallam, ya ce umurnin ya biyo bayan sabon farashin sauyin farashin mai da kamfanin PPMC, mai hakkin sanya farashin mai.

A cewarsa, wannan mataki da suka zamu ya yi daidai da jawabin gwamnati cewa za ta rika canza farashin mai wata-wata dangane da yadda farashin ya canza a kasuwar duniya.

Dan Mallam ya hakaito jawabin PPMC inda ta ce an kara farashin kayan mai zuwa N138.62 ga lita a depot.

Ya ce tuni Depot sun fara sayar musu a farashin N139.5.

Saboda haka, ya umurci dukkan mambobin kungiyar IPMAN dake karkashinsa su fara sayar da litan mai kuma a tabbatar da cewa "kada wanda ya sayar da mai fiye da N150 ga lita."

IPMAN ta umurci gidajen mai su fara sayar da mai a farashin N150
IPMAN ta umurci gidajen mai su fara sayar da mai a farashin N150
Asali: UGC

KU KARANTA: Yan ta'addan Al-Qa'ida sun fara shiga jihohin Arewa maso yamma - Amurka ta ankarar da Buhari

Legit ta ruwaito muku cewa a ranar Talata, 4 ga watan Agusta, 2020, hukumar PPPRA mai alhakin tsaida farashin kayan mai a Najeriya ta yi karin Naira shida a kan litar man fetur.

PPPRA ta maida kudin litar man fetur N138.62 a manyan tashoshin kasar. Wannan shi ne kudin da za a saida mai kafin ayi jigilarsa zuwa gidaje a watan Agusta.

Dama can kun ji ‘yan kasuwan kasar su na kokarin ganin an maida kudin litar fetur tsakanin N149 zuwa N150 a dalilin wannan canji farashi da aka samu a tashoshi.

A farkon makon nan ne wani ‘dan kasuwa ya shaidawa jaridar Punch cewa kudin fetur zai iya komawa N150 a gidajen mai a wannan watan da aka shiga.

Mataimakin shugaban kungiyar IPMAN ta manyan masu saida mai a kasa, Abubakar Maigandi, ya ce har yanzu PPPRA ba ta sanar da su sabon farashin da aka sa ba.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng