Kotun daukaka kara ta yi fatali da karar Dino Melaye, ta jaddada nasarar Adeyemi

Kotun daukaka kara ta yi fatali da karar Dino Melaye, ta jaddada nasarar Adeyemi

Kotun daukaka kara a birnin tarayya Abuja a ranar Talata ta yi watsi da karar da Sanata Dino Melaye ya shigar na kallubalantar nasarar Sanata Smart Adeyemi a matsayin wanda ya lashe zaben sanata ta mazabar Kogi ta Yamma.

Alkallan uku dukkansu sun amince a kan watsi da dalilai bakwai da aka yi laakari da su yayin watsi da daukaka karar ta Melaye.

Kotun ta jaddada hukuncin da Kotun Zaben Majalisa da ke Abuja ta yanke a ranar 10 ga watan Yunin 2020 wacce ta tabbatar da nasarar Adeyemi kamar yadda Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta INEC ta sanar.

Kotun daukaka kara ta yi fatali da karar Dino Melaye, ta jaddada nasarar Adeyemi
Kotun daukaka kara ta yi fatali da karar Dino Melaye, ta jaddada nasarar Adeyemi. Hoto daga The Punch
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Na fi jin dadin yi wa mata da suka manyanta fyade - Mai laifi

Kazalika, kotun wacce ta farko ta yi watsi da bukatar da Adeyemi ya gabatar mata ta umurci wanda ya daukaka karar wato Melaye ya biya Adeyemi N50, 000.

Ku saurari cikaken rahoton ...

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164