Korona ta harbi sabbin mutane 664 a Najeriya

Korona ta harbi sabbin mutane 664 a Najeriya

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na tuwita tun bayan bullar annobar korona, ta sanar da cewa karin sabbin mutane 664 ne aka tabbatar da cewa kwayar cutar covid-19 ta sake harba a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC tawallafa a shafinta a daren ranar Asabar, 11 ga watan Yuli, 2020.

NCDC ta fitar da jerin jihohi da jimillar ma su dauke da kwayar cutar a kowacce jiha kamar haka;

Lagos-224

FCT-105

Edo-85

Ondo-64

Kaduna-32

Imo-27

Osun-19

Plateau-17

Oyo-17

Ogun-17

Rivers-14

Delta-11

Adamawa-10

Enugu-7

Nassarawa-6

Gombe-3

Abia-3

Ekiti-3

NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:46 na daren ranar Asabar akwai jimillar mutane 31987 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a Najeriya.

DUBA WANNAN: 'Kisan girmamawa': Wani miji ya kashe matarsa ta hanyar jefeta da duwatsu

An sallami mutane 13103 bayan an tabbatar da samun saukinsu, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 724.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel